< Hebrews 3 >
1 Wherefore, holy brethren, partakers of the heavenly calling, consider the Apostle and High Priest of our profession, Christ Jesus;
Saboda haka,’yan’uwa tsarkaka, waɗanda suke da rabo a kiran nan na sama, ku kafa tunaninku a kan Yesu, manzo da kuma babban firist wanda muke shaidawa.
2 Who was faithful to him that appointed him, as also Moses [was faithful] in all his house.
Ya yi aminci ga wanda ya naɗa shi, kamar yadda Musa ya yi aminci ga dukan gidan Allah.
3 For this [man] was counted worthy of more glory than Moses, inasmuch as he who hath built the house, hath more honor than the house.
An ga Yesu ya cancanci girma fiye da Musa, kamar yadda mai ginin gida ya fi gidan daraja.
4 For every house is built by some [man]; but he that built all things [is] God.
Gama kowane gida yana da wanda ya gina shi, amma maginin dukan abu Allah ne.
5 And Moses verily [was] faithful in all his house, as a servant, for a testimony of those things which were [afterwards] to be spoken.
Musa ya yi aminci a matsayin bawa cikin dukan gidan Allah, yana ba da shaida a kan abubuwan da za a faɗa nan gaba.
6 But Christ as a son over his own house: whose house are we, if we hold fast the confidence, and the rejoicing of the hope firm to the end.
Amma Kiristi mai aminci ne kamar ɗa a gidan Allah. Mu kuwa gidansa ne, in muka tsaya gabanmu gadi da kuma begen da muke taƙama a kai.
7 Wherefore (as the Holy Spirit saith, To-day if ye will hear his voice,
Kamar dai yadda Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Yau, in kuka ji muryarsa,
8 Harden not your hearts, as in the provocation, in the day of temptation in the wilderness:
kada ku taurare zukatanku, yadda kuka yi a tawayen nan, a lokacin gwaji a hamada,
9 When your fathers tempted me, proved me, and saw my works forty years.
inda kakanninku suka gwada ni, suka kuma gwada ni, ko da yake a cikin shekaru arba’in sun ga abin da na yi.
10 Wherefore I was grieved with that generation, and said, They do always err in [their] heart; and they have not known my ways.
Shi ya sa na yi fushi da wancan zamani, na kuma ce, ‘Kullum zukatansu a karkace suke, ba su kuma san hanyoyina ba.’
11 So I swore in my wrath, They shall not enter into my rest.)
Saboda haka na yi rantsuwa a cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
12 Take heed, brethren, lest there be in any of you an evil heart of unbelief, in departing from the living God.
Ku lura fa,’yan’uwa, cewa kada waninku yă kasance da zuciya mai zunubi marar bangaskiya da takan juye daga bin Allah mai rai.
13 But exhort one another daily, while it is called To-day; lest any of you be hardened through the deceitfulness of sin.
Sai dai ku ƙarfafa juna kullum, muddin akwai lokacin da ana ce da shi Yau, don kada waninku yă zama mai taurin zuciya ta wurin ruɗun zunubi.
14 For we are made partakers of Christ, if we hold the beginning of our confidence steadfast to the end;
Mu masu tarayya ne da Kiristi idan mun riƙe bangaskiyarmu da ƙarfi daga farko har zuwa ƙarshe.
15 While it is said, To-day if ye will hear his voice, harden not your hearts, as in the provocation.
Kamar yadda aka faɗa cewa, “Yau, in kuka ji muryarsa, kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a tawayen nan.”
16 For some, when they had heard, did provoke: yet, not all that came out of Egypt by Moses.
Su wane ne suka ji suka kuma yi tawaye? Ba su ne duk waɗanda Musa ya bi da su daga Masar ba?
17 But with whom was he grieved forty years? [was it] not with them that had sinned, whose carcasses fell in the wilderness?
Da su wane ne kuwa ya yi fushi har shekaru arba’in? Ba da waɗanda suka yi zunubi, waɗanda suka mutu a hamada ba?
18 And to whom did he swear that they should not enter into his rest, but to them that believed not?
Kuma ga su wane ne Allah ya rantse cewa ba za su taɓa shiga hutunsa ba, in ba ga marasa biyayyan nan ba?
19 So we see that they could not enter in because of unbelief.
Saboda haka mun ga cewa ba su iya shiga ba, saboda rashin bangaskiyarsu ne.