< Hebrews 11 >

1 Now faith is the substance of things hoped for, the evidence of things not seen.
Bangaskiya ita ce tabbatawar al'muran da muke begensu. Ita ce tabbatawar al'amuran da idanu basu gani.
2 For by it the elders obtained a good report.
Domin ta wurin ta ne kakanninmu suka sami yardar Allah.
3 Through faith we understand that the worlds were framed by the word of God, so that things which are seen were not made of things which appeared. (aiōn g165)
Ta wurin ta ne aka hallicci duniya da umarnin Allah, har ma abubuwan da ake gani ba'a yi su daga abubuwan da suka kasance ba. (aiōn g165)
4 By faith Abel offered to God a more excellent sacrifice than Cain, by which he obtained testimony that he was righteous, God testifying of his gifts: and by it he being dead yet speaketh.
Ta dalilin bangaskiya ne Habila ya mikawa Allah hadaya da ta fi dacewa fiye da ta Kayinu. Don haka ne kuma aka yaba masa akan cewa shi adali ne. Ya sami yardar Allah sabili da sadakarsa da ya bayar. Don haka kuma, harwayau Habila yana magana, ko da shike ya rigaya ya mutu.
5 By faith Enoch was translated, that he should not see death; and was not found, because God had translated him: for before his translation he had this testimony, that he pleased God.
Ta dalilin bangaskiya aka dauki Anuhu zuwa sama domin kar ya ga mutuwa. “Ba a same shi ba kuwa, domin Allah ya dauke shi.” Kamin a dauke shi an shaida da cewa ya faranta wa Allah zuciya.
6 But without faith [it is] impossible to please [him]: for he that cometh to God must believe that he is, and [that] he is a rewarder of them that diligently seek him.
Zai yi wuya matuka a faranta wa Allah zuciya in ba tare da bangaskiya ba. Domin ya kamata dukkan wanda zai zo ga Allah, tilas ne ya bada gaskiya da kasancewar sa, kuma shi mai sakamako ne ga dukkan masu nemansa.
7 By faith Noah, being warned by God of things not seen as yet, moved with fear, prepared an ark to the saving of his house; by which he condemned the world, and became heir of the righteousness which is by faith.
Ta dalilin bangaskiya Nuhu, ya karbi sako daga Allah akan al'amuran da ba'a gani ba, ta wurin girmamawa da rawar jiki. ya gina jirgin ruwa domin ya ceci iyalan sa. Dalilin haka kwa, Allah ya hallakar da duniya, Nuhu kwa ya gaji adalci wadda ke bisa ga bangaskiya.
8 By faith Abraham, when he was called to remove into a place which he should afterwards receive for an inheritance, obeyed; and he went out not knowing whither he was going.
Ta dalilin bangaskiya ne Ibrahim, sa'an da aka kira shi, ya yi biyayya sai ya tafi wurin da zai karba a matsayin gado. Ya kwa fita bai ma san inda za shi ba.
9 By faith he sojourned in the land of promise, as [in] a foreign country, dwelling in tabernacles with Isaac and Jacob, the heirs with him of the same promise:
Ta dalilin bangaskiya kuma ya zauna bare a kasar alkawari. Ya yi zama cikin Alfarwa tare da Ishaku da Yakubu, magadan alkawari guda tare da shi.
10 For he looked for a city which hath foundations, whose builder and maker [is] God.
Domin yana hangar birnin da ke da tushi, Birnin da mai zaiyanar sa da ginin sa shine Allah.
11 Through faith also Sarah herself received strength to conceive seed, and was delivered of a child when she was past age, because she judged him faithful who had promised.
Ta dalilin bangaskiya, Ibrahim ya sami haihuwa ko da shike shi da matarsa Saratu sun yi nisa a cikin shekaru, kuma Saratu bakarariya ce, ta kuma wuce lokacin haihuwa. Tun da shike sun amince da wanda ya yi musu alkawari mai aminci ne.
12 Therefore there sprang even from one, and him as good as dead, [so many] as the stars of the sky in multitude, and as the sand which is by the sea-shore innumerable.
Sabo da haka, ta wurin mutumin nan daya, wanda ya ke kamar matacce ne, aka haifi zuriya mai dimbin yawa, su ka yawaita kamar taurari a sama kamar yashi a bakin teku, wanda ba shi kidayuwa.
13 These all died in faith, not having received the promises, but having seen them afar off, and were persuaded of [them], and embraced [them], and confessed that they were strangers and pilgrims on the earth.
Dukkan su kuwa suka mutu a cikin bangaskiya ba tare da sun karbi alkawarin ba. Maimakon haka, sun hango, kuma sun marabcesu daga nesa, sai suka amince su baki ne kuma matafiya ne a duniya.
14 For they that say such things declare plainly that they seek a country.
Gama wadanda suka yi furci haka sun nuna a fili cewa suna bidar kasa ta kansu.
15 And truly, if they had been mindful of that [country] from whence they came, they might have had opportunity to return.
Da kamar suna tunanin kasar da suka fita daga ciki, da sun sa mi damar komawa.
16 But now they desire a better [country], that is, a heavenly: wherefore God is not ashamed to be called their God; for he hath prepared for them a city.
Amma kamar yadda yake, sun bukaci kasa mafi dacewa, wato, wadda take a sama. Saboda haka ne Allah bai ji kunyar a kira shi Allahnsu ba, da shike ya shirya birni dominsu.
17 By faith Abraham, when he was tried, offered up Isaac: and he that had received the promises offered up his only-begotten [son],
Ta dalilin bangaskiya ne Ibrahim, sa'adda aka yi masa gwaji, akan ya mika Ishaku dansa hadaya.
18 Of whom it was said, That in Isaac shall thy seed be called:
Shi ne kuwa makadaicin dansa, wanda aka yi alkawari da cewa, “Ta wurinsa ne za a kira zuriyarka.”
19 Accounting that God [was] able to raise [him] even from the dead; from whence also he received him in a figure.
Ibrahim ya yi tunani da cewa Allah na da ikon tada Ishaku ko daga cikin matattu ma, haka kuwa yake a misalce, daga matattun ne ya sake karbarsa.
20 By faith Isaac blessed Jacob and Esau concerning things to come.
Ta dalilin bangaskiya ne kuma Ishaku ya albarkaci Yakubu da Isuwa game da abubuwan da ke zuwa a gaba.
21 By faith Jacob, when he was dying, blessed both the sons of Joseph; and worshiped, [leaning] upon the top of his staff.
Dalilin bangaskiya ne Yakubu, sa'adda yake bakin mutuwa, ya albarkaci 'ya'yan Yusufu dukkansu biyu. Yakubu ya yi ibada, yana tokare a kan sandarsa.
22 By faith Joseph, when he died, made mention of the departing of the children of Israel; and gave commandment concerning his bones.
Ta dalilin bangaskiya Yusufu, sa'adda karshensa ya kusa, ya yi magana game da fitar 'ya'yan Isra'ila daga Masar har ya umarce su game da kasussuwansa.
23 By faith Moses when he was born, was hid three months by his parents, because they saw [he was] a proper child; and they were not afraid of the king's commandment.
Ta dalilin bangaskiya Musa, sa'adda aka haife shi, iyayensa suka 'boye shi kimanin watanni uku domin kyakkyawan yaro ne shi, kuma basu ji tsoron dokar sarki ba.
24 By faith Moses, when he had come to years, refused to be called the son of Pharaoh's daughter;
Ta dalilin bangaskiya ne kuma Musa, sa'adda ya girma, yaki a kira shi 'dan diyar Fir'auna.
25 Choosing rather to suffer affliction with the people of God, than to enjoy the pleasures of sin for a season;
A maimakon haka, ya amince ya sha azaba tare da jama'ar Allah, a kan shagali da annashuwar zunubi na karamin lokaci.
26 Esteeming the reproach of Christ greater riches than the treasures of Egypt: for he had respect to the recompense of the reward.
Ya fahimci cewa wulakanci domin bin Almasihu babbar wadata ce fiye da dukiyar Masar. Gama ya kafa idanunsa a kan sakamakon da ke gaba.
27 By faith he forsook Egypt, not fearing the wrath of the king: for he endured, as seeing him who is invisible.
Ta dalilin bangaskiya Musa ya bar Masar. Bai ji tsoron fushin sarki ba, ya jure kamar yana ganin wannan da ba a iya ganinsa
28 Through faith he kept the passover, and the sprinkling of blood, lest he that destroyed the first-born should touch them.
Ta dalilin bangaskiya ya yi idin ketarewa da kuma yayyafa jini, domin kada mai hallaka 'ya'yan fari ya taba 'ya'yan fari na Isra'ila.`
29 By faith they passed through the Red sea as by dry [land]: which the Egyptians essaying to do were drowned.
Ta dalilin bangaskiya suka haye baharmaliya kamar bushashiyar kasa. Sa'adda Masarawa su ka yi kokarin hayewa, bahar din ta hadiye su.
30 By faith the walls of Jericho fell down after they had been encompassed seven days.
Ta dalilin bangaskiya ganuwar Yeriko ta fadi, bayan sun kewaya ta har kwana bakwai.
31 By faith the harlot Rahab perished not with them that believed not, as she had received the spies with peace.
Ta dalilin bangaskiya Rahab karuwan nan bata hallaka tare da marasa biyayya ba, don ta saukar da masu leken asirin kasa a gidanta, ta kuma sallame su lafiya.
32 And what shall I say more? for the time would fail me to tell of Gideon, and [of] Barak, and [of] Samson, and [of] Jephthah, [of] David also, and Samuel, and [of] the prophets:
Me kuma za mu ce? Gama lokaci zai kasa mini idan zan yi magana game da Gidiyon, Barak, Samson, Yefta, Dauda, Sama'ila, da annabawa.
33 Who through faith subdued kingdoms, wrought righteousness, obtained promises, stopped the mouths of lions,
Ta dalilin bangaskiya suka ci nasara kan kasashe, suka yi aikin adalci, sa'annan suka karbi alkawura. Suka rufe bakin zakuna,
34 Quenched the violence of fire, escaped the edge of the sword, out of weakness were made strong, became valiant in fight, turned to flight the armies of the aliens.
suka kashe karfin wuta, suka tsira daga bakin takobi, suka sami warkaswa daga cutattuka, suka zama jarumawan yaki, sa'annan suka ci nasara akan rundunar sojojin al'ummai.
35 Women received their dead raised to life again: and others were tortured, not accepting deliverance; that they might obtain a better resurrection:
Mata kuwa suka karbi matattunsu da aka tayar daga mutuwa. Aka azabtar da wadansu, ba su nemi yancin kansu ba, domin suna begen tashi daga mattatu.
36 And others had trial of [cruel] mockings and scourgings, and, moreover of bonds and imprisonment:
Wadansu kuwa suka sha ba'a da duka da bulala, har ma da sarka da kurkuku.
37 They were stoned, they were sawn asunder, were tempted, were slain with the sword: they wandered about in sheep-skins, and goat-skins; being destitute, afflicted, tormented;
A ka jejjefe su. Aka tsaga su kashi biyu da zarto. A ka karkashe su da takobi. Su na yawo sanye da buzun tumakai da na awaki, suka yi hijira, suka takura, suka wulakantu.
38 (Of whom the world was not worthy: ) they wandered in deserts, and [in] mountains, and [in] dens and caves of the earth.
Duniya ma ba ta dauke su a matsayin komai ba. Suka yi ta yawo a jazza, da duwatsu, da kogwanni, da kuma ramummuka.
39 And these all, having obtained a good report through faith, received not the promise:
Ko da yake mutanen nan amintattun Allah ne domin bangaskiyarsu, basu karbi cikar alkawarin ba tukunna.
40 God having provided some better [thing] for us, that they without us should not be made perfect.
Domin Allah ya shirya mana wani abu mafi kyau ba kuwa za su kammala ba sai tare da mu.

< Hebrews 11 >