< Genesis 45 >
1 Then Joseph could not refrain himself before all them that stood by him; and he cried, Cause every man to go out from me: and there stood no man with him, while Joseph made himself known to his brethren.
Yusuf bai ƙara iya daurewa a gaban dukan masu yi masa hidima ba, sai ya yi kuka da ƙarfi ya ce, “Kowa yă tashi daga gabana!” Saboda haka ba kowa a wurin sa’ad da Yusuf ya sanar da kansa ga’yan’uwansa.
2 And he wept aloud; and the Egyptians and the house of Pharaoh heard.
Sai ya yi kuka da ƙarfi har Masarawa suka ji, har labarin ya kai gidan Fir’auna.
3 And Joseph said to his brethren, I [am] Joseph; doth my father yet live? And his brethren could not answer him; for they were troubled at his presence.
Yusuf kuwa ya ce wa’yan’uwansa, “Ni ne Yusuf! Mahaifina yana nan da rai har yanzu?” Amma’yan’uwansa ba su iya amsa masa ba, gama sun firgita ƙwarai a gabansa.
4 And Joseph said to his brethren, Come near to me, I pray you: and they came near. And he said, I [am] Joseph your brother, whom ye sold into Egypt.
Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ku zo kusa da ni.” Da suka yi haka, sai ya ce, “Ni ne ɗan’uwanku Yusuf, wannan da kuka sayar zuwa Masar!
5 Now therefore be not grieved, nor angry with yourselves, that ye sold me hither; for God sent me before you to preserve life.
Yanzu dai, kada ku damu, kada kuma ku yi fushi da kanku saboda kun sayar da ni a nan, gama Allah ya aiko ni gabanku ne don in ceci rayuka.
6 For these two years [hath] the famine [been] in the land: and yet [there are] five years, in which [there shall] neither [be] tillage nor harvest.
Ga shi shekaru biyu ke nan ake yunwa a ƙasar, kuma da sauran shekara biyar masu zuwa da ba za a yi noma ko girbi ba.
7 And God sent me before you, to preserve for you a posterity in the earth, and to save your lives by a great deliverance.
Amma Allah ya aiko ni gabanku ne don in adana muku raguwa a duniya, in kuma ceci rayukanku ta wurin ceto mai girma.
8 So now [it was] not you [that] sent me hither, but God: and he hath made me a father to Pharaoh, and lord of all his house, and a ruler throughout all the land of Egypt.
“Saboda haka fa, ba ku ba ne kuka aiko ni nan, Allah ne. Ya mai da ni mahaifi ga Fir’auna, shugaban dukan gidansa da kuma mai mulkin dukan Masar.
9 Haste ye, and return to my father, and say to him, Thus saith thy son Joseph, God hath made me lord of all Egypt; come down to me; delay not:
Yanzu sai ku gaggauta zuwa wurin mahaifina ku faɗa masa, ‘Abin da ɗanka Yusuf ya ce; Allah ya mai da ni shugaban dukan Masar. Gangaro wurina; kada ka jinkirta.
10 And thou shalt dwell in the land of Goshen, and thou shalt be near to me, thou, and thy children, and thy children's children, and thy flocks, and thy herds, and all that thou hast:
Za ka yi zama a yankin Goshen, ka kasance kusa da ni. Kai,’ya’yanka da kuma jikokinka, garkunanka da shanunka, da kuma dukan abin da kake da shi.
11 And there will I nourish thee, (for yet [there are] five years of famine, ) lest thou, and thy household, and all that thou hast, should come to poverty.
Zan tanada maka a nan, domin akwai saura shekaru biyar na yunwa masu zuwa. In ba haka ba, kai da gidanka da dukan mallakarka za ku zama gajiyayyu.’
12 And behold, your eyes see, and the eyes of my brother Benjamin, that [it is] my mouth that speaketh to you.
“Ku kanku kun gani, haka ma ɗan’uwana Benyamin, cewa tabbatacce ni ne nake magana da ku.
13 And ye shall tell my father of all my glory in Egypt, and of all that ye have seen: and ye shall haste, and bring down my father hither.
Faɗa wa mahaifina game da dukan girman da aka ba ni a Masar, da kuma game da kome da kuka gani. Ku kuma kawo mahaifina a nan da sauri.”
14 And he fell upon his brother Benjamin's neck, and wept; and Benjamin wept upon his neck.
Sa’an nan ya rungume ɗan’uwansa Benyamin ya yi kuka, sai Benyamin ya rungume shi yana kuka.
15 Moreover, he kissed all his brethren, and wept upon them: and after that his brethren talked with him.
Ya sumbaci dukan’yan’uwansa, ya kuma yi kuka a kansu. Bayan haka sai’yan’uwansa suka yi masa magana.
16 And the fame of this was heard in Pharaoh's house, saying, Joseph's brethren are come: and it pleased Pharaoh well, and his servants.
Sa’ad da labarin ya kai fadan Fir’auna cewa’yan’uwan Yusuf sun zo, sai Fir’auna da dukan hafsoshin suka ji daɗi.
17 And Pharaoh said to Joseph, Say to thy brethren, This do ye; load your beasts, and go, return to the land of Canaan;
Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Faɗa wa’yan’uwanka, ‘Yi wannan; ku jibge dabbobinku ku koma zuwa ƙasar Kan’ana,
18 And take your father, and your households, and come to me: and I will give you the good of the land of Egypt, and ye shall eat the fat of the land.
Ku kawo mahaifinku da iyalanku zuwa wurina. Zan ba ku mafi kyau na ƙasar Masar, za ku kuwa ci moriyar ƙasar.’
19 Now thou art commanded, this do ye; take for yourselves wagons from the land of Egypt for your little ones, and for your wives, and bring your father, and come.
“An kuma umarce ka, ka faɗa musu, ‘Ku yi wannan, ku ɗauki wagonu daga Masar domin’ya’yanku da matanku, ku ɗauki mahaifinku ku zo.
20 Also regard not your furniture; for the good of all the land of Egypt [is] yours.
Kada ku damu da mallakarku, gama mafi kyau na Masar za su zama naku.’”
21 And the children of Israel did so: and Joseph gave them wagons, according to the commandment of Pharaoh, and gave them provision for the way.
Sai’ya’yan Isra’ila maza suka yi haka. Yusuf ya ba su wagonu kamar yadda Fir’auna ya umarta, ya kuma ba su guzuri don tafiyarsu.
22 To all of them he gave each man changes of raiment: but to Benjamin he gave three hundred [pieces] of silver, and five changes of raiment.
Ya ba da sababbin riguna ga kowannensu amma ga Benyamin ya ba shi shekel ɗari uku na azurfa da riguna kashi biyar.
23 And to his father he sent after this [manner]; ten asses laden with the good things of Egypt, and ten she-asses laden with corn and bread and meat, for his father by the way.
Ga kuma abin da ya aika wa mahaifinsa, jakuna goma da aka jibge da abubuwa mafi kyau na Masar, da jakuna mata guda goma ɗauke da hatsi da burodi da waɗansu tanade-tanade don tafiyarsa.
24 So he sent his brethren away, and they departed: and he said to them, See that ye contend not by the way.
Sa’an nan ya sallami’yan’uwansa, yayinda suke barin wurin ya ce musu, “Kada ku yi faɗa a hanya!”
25 And they went up from Egypt, and came into the land of Canaan, to Jacob their father,
Saboda haka suka haura, suka fita daga Masar, suka zo wurin maihaifinsu Yaƙub a ƙasar Kan’ana.
26 And told him, saying, Joseph [is] yet alive, and he [is] governor over all the land of Egypt. And Jacob's heart fainted, for he believed them not.
Suka faɗa masa, “Yusuf yana da rai! Gaskiya, shi ne mai mulkin dukan Masar.” Gaban Yaƙub ya fāɗi, domin bai gaskata su ba.
27 And they told him all the words of Joseph, which he had said to them: and when he saw the wagons which Joseph had sent to carry him, the spirit of Jacob their father revived:
Amma sa’ad da suka faɗa masa kome da Yusuf ya faɗa musu, da kuma sa’ad da ya ga wagonun da Yusuf ya aika don a ɗauke shi a kai da shi can, sai ya farfaɗo, ya dawo cikin hankalinsa.
28 And Israel said, [It is] enough; Joseph my son [is] yet alive: I will go and see him before I die.
Sai Yaƙub ya ce, “Na yarda! Ɗana Yusuf yana da rai har yanzu. Zan tafi in gan shi kafin in mutu.”