< Genesis 21 >
1 And the LORD visited Sarah as he had said, and the LORD did to Sarah as he had spoken.
Ana nan sai Ubangiji ya nuna wa Saratu alheri kamar yadda ya ce, Ubangiji kuma ya yi wa Saratu abin da ya yi alkawari.
2 For Sarah conceived and bore Abraham a son in his old age, at the set time of which God had spoken to him.
Saratu ta yi ciki, ta kuma haifa wa Ibrahim ɗa a tsufansa; a daidai lokacin da Allah ya yi masa alkawari.
3 And Abraham called the name of his son that was born to him, whom Sarah bore to him, Isaac.
Ibrahim ya sa wa ɗan da Saratu ta haifa masa suna Ishaku.
4 And Abraham circumcised his son Isaac, being eight days old, as God had commanded him.
Sa’ad da ɗansa Ishaku ya kai kwana takwas da haihuwa, sai Ibrahim ya yi masa kaciya, kamar yadda Allah ya umarce shi.
5 And Abraham was a hundred years old, when his son Isaac was born to him.
Ibrahim yana da shekara ɗari, sa’ad da aka haifa masa ɗansa Ishaku.
6 And Sarah said, God hath made me to laugh, [so that] all that hear will laugh with me.
Saratu ta ce, “Allah ya sa na yi dariya, kuma duk wanda ya ji game da wannan, zai yi dariya tare da ni.”
7 And she said, Who would have said to Abraham, that Sarah shall nurse children? for I have borne him a son in his old age.
Ta kuma ƙara da cewa, “Dā, wa zai iya ce wa Ibrahim, Saratu za tă yi renon yara? Duk da haka na haifar masa ɗa cikin tsufansa.”
8 And the child grew, and was weaned: and Abraham made a great feast the day that Isaac was weaned.
Yaron ya yi girma, aka kuma yaye shi, a ranar da aka yaye shi kuwa, Ibrahim ya yi babban biki.
9 And Sarah saw the son of Hagar the Egyptian, which she had borne to Abraham, mocking.
Amma Saratu ta ga cewa yaron da Hagar, mutuniyar Masar ta haifa wa Ibrahim yana wa ɗanta Ishaku gori,
10 Wherefore, she said to Abraham, Cast out this bond-woman, and her son: for the son of this bond-woman shall not be heir with my son, [even] with Isaac.
sai ta ce wa Ibrahim, “Ka kori baiwan nan tare da ɗanta, saboda ɗan baiwan nan ba zai taɓa raba gādo da ɗana Ishaku ba.”
11 And the thing was very grievous in Abraham's sight, because of his son.
Al’amarin ya ɓata wa Ibrahim rai sosai domin zancen ya shafi ɗansa.
12 And God said to Abraham, Let it not be grievous in thy sight, because of the lad, and because of thy bond-woman; in all that Sarah hath said to thee, hearken to her voice: for in Isaac shall thy seed be called.
Amma Allah ya ce wa Ibrahim, “Kada hankalinka yă tashi game da yaron nan da kuma baiwarka. Ka saurari duk abin da Saratu ta faɗa maka, saboda ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.
13 And also of the son of the bond-woman will I make a nation, because he [is] thy seed.
Zan ba ɗan baiwan nan al’umma shi ma, domin shi zuriyarka ne.”
14 And Abraham rose early in the morning, and took bread, and a bottle of water, and gave [it] to Hagar (putting [it] on her shoulder) and the child, and sent her away; and she departed, and wandered in the wilderness of Beer-sheba.
Kashegari da sassafe sai Ibrahim ya ɗauki abinci da salkar ruwa, ya ba wa Hagar. Ya ɗora su a kafaɗunta, sa’an nan ya sallame ta da yaron. Ta kama hanyarta ta kuma yi ta yawo a cikin jejin Beyersheba.
15 And the water was spent in the bottle, and she cast the child under one of the shrubs.
Sa’ad da ruwan da yake cikin salkan ya ƙare, sai ta ajiye yaron a ƙarƙashin wani ƙaramin itace.
16 And she went, and sat her down over against [him], a good way off, as it were a bow-shot: for she said, Let me not see the death of the child. And she sat over against [him], and raised her voice, and wept.
Sai ta tafi, ta zauna ɗan nesa da yaron, misalin nisan harbin baka, gama ta yi tunani ta ce, “Ba zan iya kallon yaron yana mutuwa ba.” Da ta zauna nesa da yaron, sai ta fara kuka.
17 And God heard the voice of the lad: and the angel of God called to Hagar out of heaven, and said to her, What aileth thee, Hagar? fear not; for God hath heard the voice of the lad where he [is].
Allah kuwa ya ji yaron yana kuka, sai mala’ikan Allah ya kira Hagar daga sama ya ce mata, “Mene ne damuwarki, Hagar? Kada ki ji tsoro, Allah ya ji yaron yana kuka yayinda yake kwance a can.
18 Arise, lift up the lad, and hold him in thy hand: for I will make him a great nation.
Ki ɗaga yaron ki riƙe shi a hannu, gama zan mai da shi al’umma mai girma.”
19 And God opened her eyes, and she saw a well of water: and she went, and filled the bottle with water, and gave the lad drink.
Sa’an nan Allah ya buɗe idanunta ta ga wata rijiyar ruwa. Don haka sai ta tafi ta cika salkan da ruwa, ta kuma ba wa yaron ruwa ya sha.
20 And God was with the lad; and he grew, and dwelt in the wilderness, and became an archer.
Allah ya kasance da yaron, yayinda yake girma. Ya yi zama a jeji, ya kuma zama maharbi.
21 And he dwelt in the wilderness of Paran: and his mother took for him a wife out of the land of Egypt.
Yayinda yake zama a Jejin Faran, sai mahaifiyarsa ta samo masa mata daga Masar.
22 And it came to pass at that time, that Abimelech, and Phichol the chief captain of his host, spoke to Abraham, saying, God [is] with thee in all that thou doest:
A lokacin nan Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka zo suka ce wa Ibrahim, “Allah yana tare da kai a ko mene ne kake yi.
23 Now therefore swear to me here by God, that thou wilt not deal falsely with me, nor with my son, nor with my son's son: [but] according to the kindness that I have done to thee, thou shalt do to me, and to the land in which thou hast sojourned.
Yanzu ka rantse mini a nan a gaban Allah cewa, ba za ka yaudare ni ko’ya’yana ko kuma zuriyata ba. Ka nuna mini alheri, kai da ƙasar da kake zama baƙunci kamar yadda na nuna maka.”
24 And Abraham said, I will swear.
Ibrahim ya ce, “Na rantse.”
25 And Abraham reproved Abimelech, because of a well of water, which Abimelech's servants had violently taken away.
Sa’an nan Ibrahim ya kawo kuka ga Abimelek game da rijiyar ruwan da bayin Abimelek suka ƙwace.
26 And Abimelech said, I know not who hath done this thing: neither didst thou tell me, neither yet have I heard [of it], but to-day.
Sai Abimelek ya ce, “Ban san wanda ya yi wannan ba. Ba ka faɗa mini ba, ban kuwa taɓa ji ba, sai yau.”
27 And Abraham took sheep and oxen, and gave them to Abimelech: and both of them made a covenant.
Sai Ibrahim ya kawo tumaki da shanu ya ba wa Abimelek, sai su biyun suka yi yarjejjeniya.
28 And Abraham set seven ewe-lambs of the flock by themselves.
Ibrahim ya ware’yan raguna bakwai daga cikin garke,
29 And Abimelech said to Abraham, What [mean] these seven ewe-lambs, which thou hast set by themselves?
sai Abimelek ya ce wa Ibrahim, “Mene ne ma’anar’yan raguna bakwai da ka keɓe?”
30 And he said, For [these] seven ewe-lambs shalt thou take from my hand, that they may be a witness to me, that I have digged this well.
Ibrahim ya amsa ya ce, “Ka karɓi waɗannan’yan tumaki bakwai daga hannuna a matsayin shaida cewa ni ne na haƙa wannan rijiya.”
31 Wherefore he called that place Beer-sheba: because there they swore both of them.
Saboda haka aka kira wurin Beyersheba, domin a nan ne su biyun suka yi rantsuwa.
32 Thus they made a covenant at Beer-sheba: Then Abimelech arose, and Phichol the chief captain of his host, and they returned into the land of the Philistines.
Bayan da aka yi yarjejjeniya a Beyersheba, sai Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka koma ƙasar Filistiyawa.
33 And [Abraham] planted a grove in Beer-sheba, and called there on the name of the LORD, the everlasting God.
Sai Ibrahim ya shuka itacen tsamiya a Beyersheba, a can kuma ya kira bisa sunan Ubangiji, Allah Madawwami.
34 And Abraham sojourned in the land of the Philistines many days.
Ibrahim kuwa ya zauna a ƙasar Filistiyawa na dogon lokaci.