< Ephesians 5 >
1 Be ye therefore followers of God, as dear children;
Saboda haka ku zama masu koyi da Allah, kamar kaunatattun 'ya'yansa.
2 And walk in love, as Christ also hath loved us, and hath given himself for us an offering and a sacrifice to God for a sweet-smelling savor.
Ku yi zama cikin kauna kamar yadda Almasihu ya kaunace mu, ya kuma mika kansa sadaka da hadaya ga Allah dominmu, hadaya mai kanshi abin karba ga Allah.
3 But lewdness and all uncleanness or covetousness, let it not be once named among you, as becometh saints;
Fasikanci ko kowacce irin kazamta, ko kazamar lalata kada a ambace su a tsakaninku, don haka ya dace ga masu bi.
4 Neither filthiness, nor foolish talking, nor jesting, which are not convenient: but rather giving of thanks.
Kada a ambaci batsa, maganar wauta ko alfasha wadanda ba su dace ba. Maimakon haka, mu zama masu godiya.
5 For this ye know, that no lewd, nor unclean person, nor covetous man, who is an idolater, hath any inheritance in the kingdom of Christ and of God.
Domin wannan kun sani cewa ba fasiki, ko mara tsarki, ko mai hadama wato mai bautar gumaka zai sami gado cikin mulkin Almasihu da Allah.
6 Let no man deceive you with vain words: for because of these things cometh the wrath of God upon the children of disobedience.
Kada kowa ya rude ku da maganganun wofi. Saboda wadannan abubuwa ne fushin Allah ke zuwa kan kangararrun 'ya'ya.
7 Be ye not therefore partakers with them.
Kada ku yi tarayya tare da su.
8 For ye were sometime darkness, but now [are ye] light in the Lord: walk as children of light;
Domin da ku duhu ne, amma yanzu ku haske ne cikin Ubangiji. Sai ku yi tafiya kamar 'ya'yan haske.
9 (For the fruit of the Spirit [is] in all goodness, and righteousness, and truth; )
Saboda amfanin haske shine dukan alheri, adalci da gaskiya.
10 Proving what is acceptable to the Lord.
Kuna bidar abin da Ubangiji ke murna da shi.
11 And have no fellowship with the unfruitful works of darkness, but rather reprove [them].
Kada ku sa hannu ga ayyuka marasa amfani da ayyukan duhu amma gara a tone su.
12 For it is a shame even to speak of those things which are done by them in secret.
Don abubuwan da suke yi a boye abin kunya ne a bayyana su.
13 But all things that are reproved, are made manifest by the light: for whatever doth make manifest is light.
Dukan abu, idan haske ya bayyana su, za a gan su.
14 Wherefore he saith, Awake, thou that sleepest, and arise from the dead, and Christ will give thee light.
Domin duk abin da aka bayyana ya zama haske. Saboda haka aka ce, “Ka farka, kai mai barci, ka tashi daga cikin matattu; Almasihu kuwa zai haskaka bisanka”.
15 See then that ye walk circumspectly, not as fools, but as wise,
Saboda haka, ku maida hankali yadda kuke rayuwar ku, ba kamar mutane marasa hikima ba amma kamar masu hikima.
16 Redeeming the time, because the days are evil.
Ku yi lura yadda kuke amfani da lokaci don kwanakin miyagu ne.
17 Wherefore be ye not unwise, but understanding what the will of the Lord [is].
Kada ku zama wawaye. Maimakon haka, ku fahimci ko menene nufin Ubangiji.
18 And be not drunk with wine, in which is excess; but be filled with the Spirit;
Kuma Kada ku bugu da ruwan inabi, don yana iya lalata rayuwa. Maimakon haka, ku cika da Ruhu Mai Tsarki.
19 Speaking to yourselves in psalms, and hymns, and spiritual songs, singing and making melody in your heart to the Lord,
Kuna magana da junanku cikin zabura da wakoki da wakokin ruhaniya, kuna rairawa da yabo da zuciyarku ga Ubangiji.
20 Giving thanks always for all things to God and the Father, in the name of our Lord Jesus Christ;
Kullum kuna ba da gaskiya domin dukan abubuwa cikin sunan Ubangiji Yesu ga Allah Uba.
21 Submitting yourselves one to another in the fear of God.
Kuna sarayadda kanku ga juna cikin girmama Almasihu.
22 Wives, submit yourselves to your own husbands, as to the Lord.
Mata, ku yi biyayya ga mazan ku kamar ga Ubangiji.
23 For the husband is the head of the wife, even as Christ is the head of the church: and he is the Savior of the body.
Domin miji shine shugaban matarsa kamar yadda Almasihu yake shugaban ikilisiya. Shine kuma mai ceton jiki.
24 Therefore as the church is subject to Christ, so [let] wives [be] to their own husbands in every thing.
Amma kamar yadda ikilisiya take biyayya ga Almasihu, haka kuma dole mata suyi ga mazajen su cikin kowanne abu.
25 Husbands, love your wives, even as Christ also loved the church, and gave himself for it;
Mazaje, ku kaunaci matanku kamar yadda Almasihu ya kaunaci ikilisiya har ya ba da kansa dominta,
26 That he might sanctify and cleanse it with the washing of water by the word,
Ya yi wannan domin ya tsarkake ta. Ya wanke mu da ruwan wanki ta wurin kalma.
27 That he might present it to himself a glorious church, not having spot or wrinkle, or any such thing; but that it should be holy and without blemish.
Ya yi wannan domin ya mika ma kansa ikilisiya mai daraja, ba tare da tabo ko cikas ko wani abu kamar wadannan, amma ta zama da tsarki da kuma mara aibi.
28 So ought men to love their wives, as their own bodies. He that loveth his wife, loveth himself.
Hakannan kuma, mazaje su kaunaci matansu kamar jikunnansu. Wanda yake kaunar matarsa yana kaunar kansa.
29 For no man ever yet hated his own flesh; but nourisheth and cherisheth it, even as the Lord the church:
Ba wanda ya taba kin jikinsa. Amma, yakan ciyadda shi yana kaunarsa, kamar yadda Almasihu ya kaunaci ikilisiya.
30 For we are members of his body, of his flesh, and of his bones.
Domin mu gabobin jikinsa ne.
31 For this cause shall a man leave his father and mother, and shall be joined to his wife, and they two shall be one flesh.
“Domin wannan mutum zai rabu da ubansa da uwarsa ya manne wa matarsa, su biyu su zama nama daya”.
32 This is a great mystery: but I speak concerning Christ and the church.
Wannan asirin gaskiyar, da girma yake, amma ina magana ne game da Almasihu da ikilisiyarsa.
33 Nevertheless, let every one of you in particular so love his wife even as himself: and the wife [see] that she reverence [her] husband.
Duk da haka, kowannenku dole ya kaunaci matarsa kamar kansa, matar kuma dole ta girmama mijinta.