< Acts 28 >
1 And when they had escaped, then they knew that the isle was called Melita.
Sa'adda muka sauka lafiya, sai muka ji cewa sunan tsibirin Malita.
2 And the barbarous people showed us no little kindness: for they kindled a fire, and received us every one, because of the present rain, and because of the cold.
Mutanen garin sun nuna mana alheri matuka don sun hura wuta don mu ji dimi, saboda ruwan sama da sanyin da ake yi.
3 And when Paul had gathered a bundle of sticks, and laid [them] on the fire, there came a viper out of the heat, and fastened on his hand.
Amma sa'adda Bulus ya tara kiraruwa don hura wuta, sai maciji saboda zafin wuta, ya fito ya nade hannuwansa.
4 And when the barbarians saw the animal hang on his hand, they said among themselves, No doubt this man is a murderer, whom, though he hath escaped the sea, yet vengeance suffereth not to live.
Da mazaunan garin suka ga maciji ya nade hannuwansa, sai suka cema junansu, “Ba shakka wannan mutumin mai kisan kai ne, koda shike ya tsira daga Teku, sharia baza ta barshi da rai ba”.
5 And he shook off the animal into the fire, and felt no harm.
Amma ya karkade macijin cikin wuta ba tare da ya cutar da shi ba.
6 Yet they looked when he would have swelled, or fallen down dead suddenly: but after they had looked a great while, and saw no harm come to him, they changed their minds, and said that he was a god.
Sun saurara su gani ko zai kumbura ko ya fadi matacce. Amma da suka jira dan lokaci basu ga wata matsala ta same shi ba sai suka canza tunaninsu sukace shi wani allah ne.
7 In the same quarters were possessions of the chief man of the isle, whose name was Publius; who received us, and lodged us three days courteously.
A kusa da wannan wurin tsibirin akwai wasu gonakin wani babban mutumin tsibirin, mai suna Babiliyas. Ya karbe mu ya biya bukatun mu har kwana uku.
8 And it came to pass that the father of Publius lay sick with a fever, and a bloody-flux: to whom Paul entered in, and prayed, and laid his hands on him, and healed him.
Ana nan ashe mahaifin Babiliyas yana fama da zazzabi da atuni. Bulus ya shiga, yayi masa addu'a, ya dibiya masa hannu, ya sami warkarwa.
9 So when this was done, others also who had diseases in the isle, came, and were healed:
Sa'adda wannan ya faru, sauran marasa lafiya da ke tsibirin sun zo sun sami warkarwa.
10 Who also honored us with many honors; and when we departed, they laded [us] with such things as were necessary.
Mutanen sun mutunta mu kwarai. Yayin da muke shirin tafiya, sun bamu duk abinda muke bukata.
11 And after three months we departed in a ship of Alexandria, which had wintered in the isle, whose sign was Castor and Pollux.
Bayan watanni uku, mun shiga jirgin Iskandariya wanda tun da hunturu yake a tsibirin mai zane kamannin Tagwaye Maza.
12 And landing at Syracuse, we tarried [there] three days.
Bayan saukar mu a birnin Sirakus, mun yi kwana uku a wurin.
13 And from thence we made a circuit, and came to Rhegium: and after one day the south wind blew, and we came the next day to Puteoli:
Daga nan sai muka tafi, har muka zo birnin Rigiyum. Bayan kwana daya iska mai karfi daga kudu ta taso, a cikin kwana biyu muka iso Butiyoli.
14 Where we found brethren, and were desired to tarry with them seven days: and so we went towards Rome.
A can muka iske wasu 'yan'uwa suka roke mu mu zauna tare da su har kwana bakwai. Ta wannan hanyar ce muka zo Roma.
15 And from thence when the brethren heard of us, they came to meet us as far as Appii-forum, and the Three taverns: whom when Paul saw, he thanked God, and took courage.
Daga can da 'yan'uwa suka ji labarin mu, suka fito don su tarbe mu tun daga Kasuwar Abiyas da kuma Rumfuna Uku. Da Bulus ya gan su, ya yi wa Allah godiya ya kuma sami karfafawa.
16 And when we came to Rome, the centurion delivered the prisoners to the captain of the guard: but Paul was suffered to dwell by himself, with a soldier that kept him.
Sa'adda muka shiga Roma, aka yardar wa Bulus ya zauna shi kadai tare da sojan da ke tsaronsa.
17 And it came to pass, that after three days, Paul called together the chief of the Jews. And when they were assembled, he said to them, Men, brethren, though I have committed nothing against the people, or customs of our fathers, yet I was delivered prisoner from Jerusalem into the hands of the Romans.
Ana nan bayan kwana uku, Bulus ya kira shugabannin Yahudawa. Bayan da suka taru, sai ya ce masu, “Yan'uwa, ko da shike ban yi wa kowa laifi ko keta al'adun Ubanninmu ba, duk da haka an bashe ni daurarre tun daga Urushalima zuwa ga hannunwan mutanen Roma.
18 Who when they had examined me, would have let [me] go, because there was no cause of death in me.
Bayan tuhumata, sun yi kudirin saki na, domin ban yi laifin da ya cancanci mutuwa ba.
19 But when the Jews spoke against [it], I was constrained to appeal to Cesar; not that I had aught to accuse my nation of.
Amma da Yahudawa suka tsaya a kan ra'ayin su, ya zama dole in daukaka kara zuwa ga Kaisar, ba domin ina da wani dalilin da zan yi karar al'ummata ba ne.
20 For this cause therefore have I called for you, to see [you], and to speak with [you]: because that for the hope of Israel I am bound with this chain.
Saboda wannan ne na bukaci ganinku in yi magana da ku. Saboda begen da Isra'ila suke da shi ya sa nake daure da wannan sarkar”.
21 And they said to him, We have neither received letters from Judea concerning thee, neither have any of the brethren that came shown or spoken any harm of thee.
Sai suka ce masa, “Bamu karbi wasiku daga Yahudiya game da kai ba, babu kuma wani daga cikin 'yan'uwa wanda ya kawo mana wani rahoto ko wata magana game da kai.
22 But we desire to hear from thee, what thou thinkest: for as concerning this sect, we know that every where it is spoken against.
Amma muna so mu ji daga gare ka abin da kayi tunani ka kuma gani game da wannan darikar, gama mun sani ana kushenta a ko'ina.”
23 And when they had appointed him a day, there came many to him into [his] lodging; to whom he expounded and testified the kingdom of God, persuading them concerning Jesus, both out of the law of Moses, and [out of] the prophets, from morning till evening.
Sa'adda suka sa masa rana, mutane da dama suka same shi a masaukinsa. Ya gabatarda zantattukan a gare su, yana tabbatar da bayyanuwar mulkin Allah. Har ya nemi ya rinjaye su a kan zancen Yesu, tun daga attaurat ta Musa zuwa litattafan annabawa, ya yi wannan tun daga safiya har yamma.
24 And some believed the things which were spoken, and some believed not.
Wasu sun kawar da shakkar abin da aka fada, amma wadansu basu gaskanta ba.
25 And when they agreed not among themselves, they departed, after Paul had spoken one word, Well spoke the Holy Spirit by Isaiah the prophet to our fathers,
Da shike ba su yarda da junansu ba, sai suka tafi bayan da Bulus ya fadi kalma daya, “Ruhu Mai Tsarki ya yi magana ta bakin annabi Ishaya zuwa ga kakanninku.
26 Saying, Go to this people, and say, Hearing ye shall hear, and shall not understand; and seeing ye shall see, and not perceive.
Ya ce, 'Jeka wurin al'umman nan ka ce, cikin ji zaku ji amma ba zaku fahimta ba; zaku gani amma ba zaku gane ba.
27 For the heart of this people is become gross, and their ears are dull of hearing, and their eyes have they closed; lest they should see with [their] eyes, and hear with [their] ears, and understand with [their] heart, and should be converted, and I should heal them.
Amma zuciyar mutanen nan ta yi kanta, kunnuwansu sun ji da kyar, sun rufe idanunsu; don kada su gani su gane, su kuma ji da kunuwansu, kuma su fahimta da zuciyarsu, domin su juyo ni kuma in warkar da su.”
28 Be it known therefore to you, that the salvation of God is sent to the Gentiles, and they will hear it.
Saboda haka, sai ku sani cewa wannan ceto na Allah an aikar da shi zuwa ga Al'ummai, za su kuma saurara.”
29 And when he had said these words, the Jews departed, and had great reasoning among themselves.
[Sa'adda ya fadi wannan zantattuka, Yahudawa suka tashi, suna gardama da junansu.]
30 And Paul dwelt two whole years in his own hired house, and received all that came in to him,
Bulus ya zauna shekaru biyu a cikin gidan hayarsa, yana marabtar duk wadanda suka zo wurinsa.
31 Preaching the kingdom of God, and teaching those things which concern the Lord Jesus Christ, with all confidence, no man forbidding him.
Yana wa'azin mulkin Allah, yana koyarwa da al'amuran Ubangiji Yesu Kristi gaba gadi. Ba wanda ya hana shi.