< Acts 25 >

1 Now when Festus had come into the province, after three days he ascended from Cesarea to Jerusalem.
Da Festas ya shiga lardin, kuma bayan kwana uku, ya tashi daga Kaisariya ya tafi Urushalima.
2 Then the high priest and the chief of the Jews informed him against Paul, and besought him,
Sai babban firist da manyan Yahudawa suka kawo wa Festas sara a kan Bulus.
3 And desired favor against him, that he would send for him to Jerusalem, laying wait in the way to kill him.
Suka roki tagomashi wurin Festas ya kira Bulus zuwa Urushalima domin su kashe shi a hanya.
4 But Festus answered, that Paul should be kept at Cesarea, and that he himself would depart shortly [thither].
Amma Festas ya amsa masu cewa, Bulus dan sarka ne a Kaisariya, kuma ba da dadewa ba shi da kansa zai koma can.
5 Let them therefore, said he, who among you are able, go down with [me], and accuse this man, if there is any wickedness in him.
“Saboda haka duk wadanda za su iya, su biyo mu. Idan akwai wani laifi game da mutumin, sai ku zarge shi.”
6 And when he had tarried among them more than ten days, he went down to Cesarea; and the next day sitting on the judgment-seat, commanded Paul to be brought.
Bayan kwana takwas ko goma, sai ya gangara zuwa Kaisariya. Washegari ya zauna bisa kursiyin shari'a ya bada umarni a kawo Bulus a gabansa.
7 And when he had come, the Jews who came down from Jerusalem stood around, and laid many and grievous complaints against Paul, which they could not prove;
Da Bulus ya iso, Yahudawa daga Urushalima suka tsaya kusa, suka yi ta kawo kararraki, amma basu iya tabbatar da su ba.
8 While he answered for himself, Neither against the law of the Jews, neither against the temple, nor yet against Cesar have I committed any offense.
Bulus ya kare kansa ya ce, “Ban yi wa kowa laifi ba, ko Yahudawa, ko haikali, ko kuma Kaisar.”
9 But Festus, willing to do the Jews a pleasure, answered Paul, and said, Wilt thou go to Jerusalem, and there be judged concerning these things before me?
Amma Festas yana neman farin jini wajen Yahudawa, sabo da haka ya tambayi Bulus ya ce, “Kana so ka je Urushalima in shari'anta ka a can game da wadannan abubuwa?”
10 Then said Paul, I stand at Cesar's tribunal, where I ought to be judged: to the Jews have I done no wrong, as thou very well knowest.
Bulus ya ce, “Ina tsaye a Ddakalin Shari'ar Kaisar inda dole a shari'anta ni. Ban yi wa Yahudawa laifi ba, kamar yadda ka sani sosai.
11 For if I am an offender, or have committed any thing worthy of death, I refuse not to die: but if there is none of these things of which these accuse me, no man may deliver me to them. I appeal to Cesar.
Idan lallai na yi laifi kuma na yi abin da ya chanchanci mutuwa, ban ki ba in mutu. Amma idan zarginsu karya ne, kada kowa ya bashe ni gare su. Ina daukaka kara zuwa ga Kaisar.”
12 Then Festus, when he had conferred with the council, answered, Hast thou appealed to Cesar? to Cesar thou shalt go.
Bayan Festas ya tattauna da majalisa ya amsa ya ce, “Kana kira ga Kaisar; za ka tafi wurin Kaisar.”
13 And after certain days, king Agrippa and Bernice came to Cesarea, to salute Festus.
Bayan wadansu kwanaki, sarki Agaribas da Barniki suka iso Kaisariya domin su ziyarci Festas.
14 And when they had been there many days, Festus declared Paul's cause to the king, saying, There is a certain man left in bonds by Felix:
Da ya kasance kwanaki da yawa, Festas ya fada wa sarki labarin Bulus ya ce, “Akwai wani mutum dan sarka da Filikus ya bari a kurkuku.
15 About whom, when I was at Jerusalem, the chief priests and the elders of the Jews informed [me], desiring [to have] judgment against him.
Sa'anda nake a Urushalima, babban firist da dattawan Yahudawa suka kawo kararsa gare ni, suka roka a kashe shi.
16 To whom I answered, It is not the manner of the Romans to deliver any man to die, before he who is accused hath the accusers face to face, and hath license to answer for himself concerning the crime laid against him.
Game da wannan na amsa na ce masu, ba al'adar Romawa ba ce a ba da mutum tagomashi; sai wanda ake kararsa an bashi zarafi ya kare kansa a gaban masu kararsa, ya kuma bada hujjojinsa game da kararakin.
17 Therefore, when they had come hither, without any delay on the morrow I sat on the judgment-seat, and commanded the man to be brought forth;
Saboda haka, da duk suka taru ban bata lokaci ba, washegari na zauna a kujerar shari'a, na ba da umarni a kawo mutumin.
18 Against whom, when the accusers stood up, they brought no accusation of such things as I supposed:
Da masu karar suka fadi kararsu, sai na fahimci karar ba wani muhimmin abu a cikinta.
19 But had certain questions against him of their own superstition, and of one Jesus who was dead, whom Paul affirmed to be alive.
Sai dai na ga cewa jayayya ce tsakanin su ta addini a kan wani Yesu da ya mutu, wanda Bulus ya ce yana da rai.
20 And because I doubted of such manner of questions, I asked [him] whether he would go to Jerusalem, and there be judged concerning these matters.
Na rasa yadda zan bincike wannan al'amarin, sai na tambaye shi ko zai je Urushalima a shari'anta shi kan wadannan abubuwa.
21 But when Paul had appealed to be reserved to the hearing of Augustus, I commanded him to be kept till I might send him to Cesar.
Amma da Bulus ya nemi a lura da shi, Kaisar ya shari'anta shi, sai na ba da umarni a ajiye shi har sai na aika shi wurin Kaisar.”
22 Then Agrippa said to Festus, I would also hear the man myself. To-morrow, said he, thou shalt hear him.
Agaribas yace wa Festas. “Zan so ni ma in saurari mutumin nan.” “Gobe za ka ji shi,” in ji Fostus.
23 And on the morrow, when Agrippa had come, and Bernice, with great pomp, and had entered into the place of hearing, with the chief captains and principal men of the city, at the command of Festus Paul was brought forth.
Washegari Agaribas da Barniki suka zo tare da kasaitaccen taro suka shiga dakin taro tare da hafsoshi da shugabanin gari. Da Festas ya ba da umarni, aka fito da Bulus wurinsu.
24 And Festus said, King Agrippa, and all men who are here present with us, ye see this man about whom all the multitude of the Jews have dealt with me, both at Jerusalem, and [also] here, crying that he ought not to live any longer.
Festas ya ce, “Sarki Agaribas da dukanku da kuke tare da mu a nan, kun ga mutumin nan, dukan Yahudawa sun gana da ni a Urushalima da nan kuma. Suna mani ihu cewa, bai chanchanta a bar shi da rai ba.
25 But when I found that he had committed nothing worthy of death, and that he himself hath appealed to Augustus, I have determined to send him.
Na gane bai yi wani abin da ya chanchanci mutuwa ba; amma saboda ya daukaka kara zuwa Kaisar, na yanke shawara in aika shi.
26 Of whom I have no certain thing to write to my lord. Wherefore I have brought him forth before you, and specially before thee, O king Agrippa, that after examination had, I may have somewhat to write.
Amma ba ni da wani dalili na musamman da zan rubuta wasika ga Kaisar. Saboda wannan dalili na kawo shi gabanku, masamman kai ya sarki Agaribas. Domin in sami karin abin da zan rubuta game da shi.
27 For it seemeth to me unreasonable to send a prisoner, and not also to signify the crimes [laid] against him.
Gama a ganina wauta ce in aika dan sarka ba tare da na rubuta laifi a kansa ba.”

< Acts 25 >