< Acts 19 >
1 And it came to pass, that while Apollos was at Corinth, Paul having passed through the upper region, came to Ephesus; and finding certain disciples,
Sa'adda Afolos yake a Koranti, Bulus ya zagaya kasar tudu ya zo birnin Afisa, a nan kuma ya sami wadansu almajirai.
2 He said to them, Have ye received the Holy Spirit since ye believed? And they said to him, We have not so much as heard whether there is any Holy Spirit.
Bulus ya ce masu, “Ko kun karbi Ruhu Mai Tsarki sa'anda kuka ba da gaskiya?” Suka amsa, “A'a bamu taba jin labarin Ruhu Mai Tsarki ba.
3 And he said to them, Into what then were ye baptized? And they said, Into John's baptism.
Bulus ya ce, “Wacce irin baftisma aka yi maku?” Suka ce, “Baftismar Yahaya”
4 Then said Paul, John verily baptized with the baptism of repentance, saying to the people, That they should believe on him who should come after him, that is, on Christ Jesus.
Bulus ya amsa ya ce, “Yahaya ya yi wa mutane baftismar tuba, ya ce su ba da gaskiya wanda zai zo bayansa, wato, Yesu kenan.”
5 When they heard [this], they were baptized into the name of the Lord Jesus.
Da mutanen suka ji haka, sai aka yi masu baftisma cikin sunan Ubangiji Yesu.
6 And when Paul had laid [his] hands upon them, the Holy Spirit came on them; and they spoke in languages, and prophesied.
Sa'adda Bulus ya dibiya hannu a kansu, Ruhu Mai Tsarki kuma ya sauka a kansu suka yi magana da harsuna da kuma annabci.
7 And all the men were about twelve.
Su wajen mutum goma sha biyu ne.
8 And he went into the synagogue, and spoke boldly for the space of three months, disputing and persuading the things concerning the kingdom of God.
Bulus ya shiga majami'a ya yi ta koyarwa gabagadi misalin tsawon wata uku. Yana bi da su cikin nazarin maganar yana fahimtar da mutane su gaskanta game da abubuwa da suka shafi mulkin Allah.
9 But when divers were hardened, and believed not, but spoke evil of that way before the multitude, he departed from them, and separated the disciples, disputing daily in the school of one Tyrannus.
Amma sa'adda wadansu Yahudawa suka taurare, suka ki yin biyayya, sai suka fara bata hanyar Almasihu a gaban taron. Saboda haka sai Bulus ya janye daga wurinsu tare da wadanda suka ba da gaskiya. Ya fara koyarwa a makarantar Tiranus.
10 And this continued for the space of two years; so that all they who dwelt in Asia heard the word of the Lord Jesus, both Jews and Greeks.
Haka ya cigaba shekaru biyu har duk mazaunan Asiya suka ji maganar Ubangiji, Yahudawa da Helenawa.
11 And God wrought special miracles by the hands of Paul:
Allah ya yi manyan al'ajibai ta hannun Bulus,
12 So that from his body were brought to the sick, handkerchiefs, or aprons, and the diseases departed from them, and the evil spirits went out of them.
har marasa lafiya suka warke, mugayen ruhohi suka fito daga cikin mutane, sa'adda suka karbi kyallaye da mayafai daga jikin Bulus.
13 Then certain of the vagabond Jews, exorcists, took upon them to call over them who had evil spirits, the name of the Lord Jesus, saying, We adjure you by Jesus whom Paul preacheth.
Amma akwai Yahudawa masu tsubu da suka biyo ta wajen, suka dauka wa kansu su yi amfani da sunan Yesu. Suka ce, “Mun dokace ku cikin sunan Yesu wanda Bulus yake wa'azinsa, ku fita.”
14 And there were seven sons of [one] Sceva a Jew, [and] chief of the priests, who did so.
Wadanda suka yi wannan su bakwai ne 'ya'yan wani babban firist Bayahude mai suna Siba.
15 And the evil spirit answered and said, Jesus I know, and Paul I know; but who are ye?
Mugun ruhun ya amsa ya ce, “Na san Yesu, na san Bulus, amma ku, su wanene?”
16 And the man in whom the evil spirit was, leaped on them, and overcame them, and prevailed against them, so that they fled out of that house naked and wounded.
Sai mugun ruhun da ke cikin mutumin ya fada a kan matsubatan ya fi karfinsu ya kuma bubuge su. Suka runtuma da gudu suka fice daga dakin tsirara da raunuka.
17 And this was known to all the Jews and Greeks also dwelling at Ephesus: and fear fell on them all, and the name of the Lord Jesus was magnified.
Wannan ya zama sanannen abu ga dukan mutane, Yahudawa da Helenawa mazaunan Afisa. Suka ji tsoro kwarai, sunan Ubangiji Yesu ya sami daukaka.
18 And many that believed came, and confessed, and showed their deeds.
Masu bi da yawa kuma, suka zo suka furta mugayen ayyukan da suka aikata.
19 Many also of them who used curious arts, brought their books together, and burned them before all [men]; and they counted the price of them, and found [it] fifty thousand [pieces] of silver.
Masu sihiri suka kawo littattafansu suka kona a gaban mutane. Da aka yi jimilar tamaninsu, aka samu sun kai dubu hamsin na azurfa.
20 So mightily grew the word of God, and prevailed.
Sai maganar Ubangiji ta yadu da iko ta hanyoyi da yawa.
21 After these things were ended, Paul purposed in the spirit, when he had passed through Macedonia, and Achaia, to go to Jerusalem, saying, After I have been there, I must also see Rome.
Da Bulus ya kammala aikinsa na bishara a Afisa, Ruhu ya bishe shi sai ya bi ta Makidoniya da Akiya a kan hanyarsa zuwa Urushalima. Ya ce, “Bayan na je can, dole in je Roma.”
22 So he sent into Macedonia two of them that ministered to him, Timothy and Erastus; but he himself stayed in Asia for a season.
Bulus ya aiki almajiransa biyu Timoti da Irastus zuwa Makidoniya, wadanda suka taimake shi. Amma shi da kansa ya jira a Asiya na dan lokaci.
23 And the same time there arose no small stir about that way.
A wannan lokacin sai aka yi babban tashin hankali a Afisa game da wannan Hanyar.
24 For a certain [man] named Demetrius, a silver-smith, who made silver shrines for Diana, brought no small gain to the artificers;
Wani Makeri mai suna Damatrayus wanda ke kera sifoffin gunkin azurfa na Dayana, wanda sana'a ce mai kawo wa makera riba sosai.
25 Whom he called together with the workmen of like occupation, and said, Sirs, ye know that by this craft we have our wealth:
Ya tattara makera ya ce da su, “Kun sa ni da wanan sana'a ne muke samun kudi mai yawa.
26 Moreover, ye see and hear, that not alone at Ephesus, but almost throughout all Asia, this Paul hath persuaded and turned away many people, saying, that they are no gods which are made with hands.
Kun gani kun kuma ji cewa, ba a Afisa kadai ba, amma har da fadin kasar Asiya wannan Bulus ya rinjayi mutane da yawa. Yana cewa babu alloli da ake kerawa da hannu.
27 So that not only this our craft is in danger to be set at naught; but also that the temple of the great goddess Diana should be despised, and her magnificence should be destroyed, whom all Asia, and the world worshipeth.
Ba sana'ar mu kadai ke cikin hatsari ba, amma har da haikalin allahnmu Dayana babba zai zama mara amfani. Ta haka za ta rasa girmanta, ita da dukan kasar Asiya da duniya ke wa sujada.”
28 And when they heard [these sayings], they were full of wrath, and cried out, saying, Great [is] Diana of the Ephesians.
Da suka ji haka sai suka fusata kwarai, suka yi kira mai karfi suna cewa “Mai girma ce Dayana ta Afisa.”
29 And the whole city was filled with confusion: and having caught Gaius and Aristarchus, men of Macedonia, Paul's companions in travel, they rushed with one accord into the theater.
Gari gaba daya ya rude, jama'a kuma sun hanzarta zuwa wurin taron. Kafin wannan lokaci, sun riga sun kama abokan tafiyar Bulus, wato Gayus da Aristakas wadanda suka zo daga Makidoniya.
30 And when Paul would have entered in to the people, the disciples suffered him not.
Bulus ya yi niyya ya shiga cikin taron jama'ar, amma almajiran suka hana shi.
31 And certain of the chief of Asia, who were his friends, sent to him, desiring [him] that he would not adventure himself into the theater.
Haka nan ma wadansu abokan Bulus da ke shugabanin yankin al'umma Asiya sun aika masa da roko mai karfi kada ya shiga dandalin.
32 Some therefore cried one thing, and some another: for the assembly was confused, and the greater part knew not why they had come together.
Wadansu mutane na kirarin wani abu, wadansu kuma na kirarin wani abu dabam, domin jama'a sun rude. Da yawa daga cikinsu ma ba su san dalilin taruwarsu ba.
33 And they drew Alexander out of the multitude, the Jews putting him forward. And Alexander beckoned with the hand, and would have made his defense to the people.
Yahudawa suka kawo Iskandari ya tsaya a gaban taruwan jama'a. Iskandari ya mika hannunsa sama domin ya yi bayani ga jama'a.
34 But when they knew that he was a Jew, all with one voice about the space of two hours cried out, Great [is] Diana of the Ephesians.
Amma da suka gane shi Bayahude ne, sai dukansu suka kwala ihu wajen sa'a biyu, “Mai girma ce Dayana ta Afisa.”
35 And when the town-clerk had appeased the people, he said, [Ye] men of Ephesus, what man is there that knoweth not that the city of the Ephesians is a worshiper of the great goddess Diana, and of the [image] which fell down from Jupiter?
Da magatakardar garin ya sha kan jama'a, sai ya ce, “Ya ku mutanen Afisa, wanene bai san cewa birnin Afisa cibiya ce na allahn nan Dayana mai girma da na sifar da ta fado daga sama ba?
36 Seeing then that these things cannot be contradicted, ye ought to be quiet, and to do nothing rashly.
Tun da ba a karyata wadannan abubuwa ba, ya kamata ku yi shuru don kada ku yi wani abu a gaggauce.
37 For ye have brought hither these men, who are neither robbers of churches, nor yet blasphemers of your goddess.
Gama kun kawo wadannan mutane a wannan dakin sharia ba a kan su mafasa ne na haikali ba ko kuma masu sabo ga allahnmu ba.
38 Wherefore, if Demetrius and the artificers who are with him, have a matter against any man, the law is open, and there are deputies: let them implead one another.
Saboda haka idan Damatrayas da makeran da ke tare da su na da wata tuhuma a kan wani, kotuna suna nan a bude masu shari'a kuma suna nan. Ba ri su kai karar junansu.
39 But if ye inquire any thing concerning other matters, it shall be determined in a lawful assembly.
Amma idan akwai maganganu na dubawa, za a daidaita su a taronmu na lokaci lokaci.
40 For we are in danger to be called in question for this day's uproar, there being no cause by which we may give an account of this concourse.
Domin hakika muna cikin hatsarin zargi game da hargitsin yau. Babu dalilin wanan yamutsi domin ba mu da bayani a kansa.”
41 And when he had thus spoken, he dismissed the assembly.
Da ya fadi haka, sai ya sallami taron.