< Acts 16 >
1 Then he came to Derbe and Lystra: and behold, a certain disciple was there, named Timothy, the son of a certain woman who was a Jewess, and believed, but his father [was] a Greek.
Bulus ya kuma isa Darbe da Listira, in da akwai wani almajiri mai suna Timoti a wurin, dan wata Bayahudiya wadda ta ba da gaskiya; ubansa kuwa Baheline ne.
2 Who was well reported of by the brethren that were at Lystra and Iconium.
Ana maganar kirki a kansa ta bakin 'yan'uwa da ke Listira da Ikoniyan.
3 Him would Paul have to go forth with him; and took and circumcised him, because of the Jews who were in those quarters: for they all knew that his father was a Greek.
Bulus ya yi wa Timoti kaciya, domin yana so su yi tafiya tare, domin kuma saboda Yahudawan da ke wurin, sun san cewa ubansa Baheline ne.
4 And as they went through the cities, they delivered to them the decrees to keep that were ordained by the apostles and elders who were at Jerusalem.
Suna shiga cikin biranen, suna yi wa iklisiyoyi gargadi da su yi biyayya da umurnan da Manzanni da dattawa suka rubuta a Urushalima.
5 And so were the churches established in the faith, and increased in number daily.
Bangaskiyar iklisiyoyi kuwa ta karu, ana kuma samun karuwa na wadanda suke ba da gaskiya kowace rana.
6 Now when they had gone throughout Phrygia, and the region of Galatia, and were forbidden by the Holy Spirit to preach the word in Asia;
Bulus da abokan aikin sa sun shiga cikin lardin Firigiya da Galatiya, tun da Ruhu Mai Tsarki ya hana su wa'azin kalmar a cikin yankin Asiya.
7 After they had come to Mysia, they essayed to go into Bithynia: but the Spirit suffered them not.
Sun zo kusa da Misiya, da nufin shiga cikin Bitiniya, Ruhun Yesu ya hana su.
8 And they, passing by Mysia, came down to Troas.
Da suka ratse ta cikin Misiya, sai suka shiga birnin Taruwasa.
9 And a vision appeared to Paul in the night: There stood a man of Macedonia, and prayed him, saying, Come over into Macedonia, and help us.
Bulus ya ga wahayi cikin dare, wani mutumin Makidoniya na kiransa, yana cewa. ''Ka zo Makidoniya ka taimake mu''.
10 And after he had seen the vision, immediately we endeavored to go into Macedonia, assuredly gathering, that the Lord had called us to preach the gospel to them.
Bulus, da ganin haka, ya kama hanya zuwa Makidoniya, da tunanin Allah ne ya ke so su kai wa mutanen Makidoniya bishara.
11 Therefore loosing from Troas, we came with a straight course to Samothracia, and the next [day] to Neapolis;
Da barin Taruwasa, Bulus da kungiyarsa sun shiga jirgin ruwa zuwa Samutaraki, da gari ya waye kuma sun tafi Niyafolis;
12 And from thence to Philippi, which is the chief city of that part of Macedonia, [and] a colony: and we were in that city abiding certain days.
Daga nan kuma suka tafi Filibi, birni na Makidoniya, mai muhimmanci ne a yankin Roma, in da mun yi zango kwanaki da dama.
13 And on the sabbath we went out of the city by a river side, where prayer was wont to be made; and we sat down, and spoke to the women who resorted [thither].
Ranar Asabaci mun je kofar gari, gefen rafi, da tunanin samun wurin addu'a. Mun zauna mun kuma yi magana da matan da sun taru a wurin.
14 And a certain woman named Lydia, a seller of purple, of the city of Thyatira, who worshiped God, heard [us]: whose heart the Lord opened, that she attended to the things which were spoken by Paul.
Wata mace mai suna Lidiya, 'yar kasuwa ce a birnin Tiyatira, mai bautar Allah ce, ta saurare mu. Ubangiji ya bude zuciyarta, ta mai da hankali ga maganar da Bulus ke fadi.
15 And when she was baptized, and her household, she besought [us], saying, If ye have judged me to be faithful to the Lord, come into my house, and abide [there]: And she constrained us.
Sa'anda da aka yi mata Baftisma tare da mutanen gidanta, ta ce da mu, “Idan kun dauke ni mai bautar Allah, ku zo gidana ku zauna.” Sai ta rinjaye mu.
16 And it came to pass as we went to prayer, a certain damsel possessed with a spirit of divination, met us, who brought her masters much gain by sooth-saying:
A daidai wannan lokaci, muna tafiya wurin addu'a, wata yarinya mai ruhun duba ta hadu da mu. Iyayen gijinta na arziki da ita sosai.
17 The same followed Paul and us, and cried, saying, These men are the servants of the most high God, who show to us the way of salvation.
Tana bin Bulus, tare da mu, tana fadi da murya mai karfi cewa, ''Wadannan mutanen, bayin Allah mafi daukaka ne, suna sanar maku hanyar ceto ne''.
18 And this she did many days. But Paul being grieved, turned and said to the spirit, I command thee in the name of Jesus Christ to come out of her. And he came out the same hour.
Ta dauki kwanaki tana haka. Amma Bulus ya yi fushi da ita ainun, ya juya ya umarci ruhun, ya ce, ''Na umarce ka, ka rabu da ita a cikin sunan Yesu Almasihu''. Ruhun ya yi biyayya ya rabu da ita nan take.
19 And when her masters saw that the hope of their gains was gone, they caught Paul and Silas, and drew [them] into the market-place to the rulers,
Da iyayengijinta suka ga cewa hanyar shigar kudinsu ta toshe, sai suka kama Bulus da Sila, suka ja su cikin kasuwa suka kai su gaban mahunkunta.
20 And brought them to the magistrates, saying, These men, being Jews, do exceedingly trouble our city,
Da suka kai su Kotu, suka ce, ''Wadannan mutane Yahudawa ne, suna kawo tashin hankali a birninmu.
21 And teach customs which are not lawful for us to receive, neither to observe, being Romans.
Suna koyar da abubuwa da ba su karbuwa a gare mu, balle mu aikata, a matsayinmu na Romawa.”
22 And the multitude rose together against them: and the magistrates rent off their clothes, and commanded to beat [them].
Sai jama'a gaba daya sun tayar wa Bulus da Sila; alkalan kuma sun yage rigunansu, sun ba da umarni a duki Bulus da Sila da bulala.
23 And when they had laid many stripes upon them, they cast [them] into prison, charging the jailer to keep them safely.
Bayan dukan, an jefa su Bulus a kurkuku, an ba mai tsaron kurkukun umurni ya kulle su da kyau, kada su gudu.
24 Who, having received such a charge, thrust them into the inner prison, and made their feet fast in the stocks.
Shi kuma ya yi hakanan, ya sa masu sarkoki a kafafun su, kamar yadda aka umurce shi.
25 And at midnight Paul and Silas prayed, and sang praises to God: and the prisoners heard them.
Da tsakar dare, Bulus da Sila suna yin adu'a, su na raira wakoki ga Allah, sauran 'yan sarkar su na jin su.
26 And suddenly there was a great earthquake, so that the foundations of the prison were shaken: and immediately all the doors were opened, and every one's bands were loosed.
Nan da nan sai ga wata girgizar kasa, wadda ta sa ginshikan kurkukun sun kadu, nan da nan kofofin kurkukun sun bude, 'yan sarka kuma, sarkokin su sun karkatse.
27 And the keeper of the prison awaking out of his sleep, and seeing the prison doors open, he drew out his sword, and would have killed himself, supposing that the prisoners had fled.
Mai tsaron kurkukun ya tashi daga barci ya ga kofofin kurkukun a bude, ya zaro takobi, zai kashe kan sa, a tunanin sa, 'yan sarkar sun gudu.
28 But Paul cried with a loud voice, saying, Do thyself no harm: for we are all here.
Amma Bulus ya ta da murya da karfi, ya ce, ''kada kayi wa kanka barna, domin dukan mu muna nan''.
29 Then he called for a light, and sprang in, and came trembling, and fell down before Paul and Silas;
Mai tsaron kurkukun ya aika a kawo fitila, ya shiga ciki a gurguje da rawan jiki, ya fadi a gaban Bulus da Sila,
30 And brought them out, and said, Sirs, what must I do to be saved?
ya fitar da su waje ya ce, ''Shugabanni, me ya kamata in yi domin in tsira?''
31 And they said, Believe on the Lord Jesus Christ, and thou shalt be saved, and thy house.
Sun ce masa, ''ka ba da gaskiya ga Yesu Ubangiji, da kai da gidan ka, za ku sami tsira''.
32 And they spoke to him the word of the Lord, and to all that were in his house.
Bulus da Sila suka fada masa maganar Ubangiji, tare da iyalinsa.
33 And he took them the same hour of the night, and washed [their] stripes; and was baptized, he and all his, without delay.
Shi mai tsaron kurkukun ya dauke su cikin daren, ya wanke raunukansu, an kuma yi masa Baftisma nan da nan tare da iyalinsa.
34 And when he had brought them into his house, he set food before them, and rejoiced, believing in God with all his house.
Ya kai Bulus da Sila gidansa, ya ba su abinci. Murna ta cika gidan mai tsaron kurkukun, domin iyalin sa duka sun ba da gaskiya ga Allah.
35 And when it was day, the magistrates sent the sergeants, saying, Let those men go.
Da gari ya waye, alkalai sun ba da sako a saki Bulus da Sila.
36 And the keeper of the prison told this saying to Paul, The magistrates have sent to let you go: now therefore depart, and go in peace.
Mai tsaron kurkukun kuwa ya sanar wa Bulus wannan magana ta alkalan, saboda haka ya ce wa Bulus, ''Ku tafi cikin salama''.
37 But Paul said to them, They have beaten us openly uncondemned, being Romans, and have cast [us] into prison; and now do they thrust us out privately? no verily; but let them come themselves and bring us out.
Amma Bulus ya ce masu, “Sun yi mana duka a fili a gaban mutane mu da muke Romawa, ba a kashe mu ba, sun kuma sa mu a kurkuku; suna koran mu a asirce? Su zo da kansu su fitar da mu.
38 And the sergeants told these words to the magistrates: and they feared when they heard that they were Romans.
Masu tsaron kurkuku sun mayar da maganar Bulus ga alkalan, wanda ya sa sun firgita, da jin cewa Bulus da Sila Romawa ne.
39 And they came and besought them, and brought [them] out, and desired [them] to depart out of the city.
Alkalai da kansu sun zo sun roki Bulus da Sila; da suka fitar da su daga kurkukun, sun ce wa Bulus da Sila su bar birnin.
40 And they went out of the prison, and entered into [the house of] Lydia: and when they had seen the brethren, they comforted them, and departed.
Da hakanan ne Bulus da Sila suka fita daga kurkuku, sun je gidan Lidiya. Da Bulus da Sila sun ga 'yan'uwa, sun karfafa su, sa'annan suka bar birnin.