< Acts 14 >

1 And it came to pass in Iconium, that they went both together into the synagogue of the Jews, and so spoke, that a great multitude both of the Jews, and also of the Greeks, believed.
A lokacin da Bulus da Barnaba sun shiga garin Ikoniya suka shiga majami'an Yahudawa suka yi wa'azi yadda har mutane da yawa daga cikin Yahudawa da Hellinawa suka ba da gaskiya.
2 But the unbelieving Jews stirred up the Gentiles, and made their minds evil-affected against the brethren.
Amma Yahudawa da basu yi biyayya ba, suka zuga al'umman har suka yi fushi da 'yan'uwan.
3 A long time therefore they abode speaking boldly in the Lord, who gave testimony to the word of his grace, and granted signs and wonders to be done by their hands.
Suka zauna a wurin na tsawon lokaci, suna yni maganarsu gabagadi da ikon Ubangiji, yana kuma shaidar sakon alherinsa. Ya yi wannan ta wurin alamu da al'ajibai ta hannun Bulus da Barnaba.
4 But the multitude of the city was divided: and part held with the Jews, and part with the apostles.
Saboda haka mutanen garin sun rabu: wadansun su suka bi ra'ayin Yahudawa, wasu kuwa sun bi manzannin.
5 And when there was an assault made both of the Gentiles, and also of the Jews, with their rulers, to use [them] despitefully, and to stone them,
Al'umman garin da Yahudawa sun nemi jan hankali shugabanninsu, don su wulakanta Bulus da Barnaba, su jajjefe su,
6 Being apprised of [it], they fled to Lystra and Derbe, cities of Lycaonia, and to the region in that vicinity.
da suka gane haka suka gudu zuwa biranen Likoniya, Listira da Darbe, da garuruwa wadanda ke kewaye da su,
7 And there they preached the gospel.
a can suka yi wa'azin bishara.
8 And there sat a certain man at Lystra, impotent in his feet, being a cripple from his mother's womb, who had never walked.
A Listira akwai wani wanda ke zaune bai taba tashi da kafafunsa ba, don shi gurgu ne tun daga haihuwa.
9 The same heard Paul speak: who steadfastly beholding him, and perceiving that he had faith to be healed,
Wannan mutumin ya ji Bulus yana magana. Bulus ya kafa masa ido, ya gane mutumin na da bangaskiya da za a warkar da shi. Sai ya ce masa da murya mai karfi, “Tashi ka tsaya akan kafafunka”
10 Said with a loud voice, Stand upright on thy feet. And he leaped and walked.
Sai mutumin ya yi tsalle ya fara tafiya da kafafunsa, yana yawo.
11 And when the people saw what Paul had done, they lifted up their voices, saying in the speech of Lycaonia, The gods have come down to us in the likeness of men.
Da jama'an garin sun ga abin da Bulus ya yi, suka tada muryarsu suna cewa da Likoniyanci, “Ai alloli sun ziyarce mu daga sama, da kamanin mutane.”
12 And they called Barnabas, Jupiter, and Paul, Mercurius, because he was the chief speaker.
Suna kiran Barnaba da sunan “Zafsa,” Bulus kuwa suka kira shi da sunan “Hamisa” domin shine yafi yin magana.
13 Then the priest of Jupiter, who was before their city, brought oxen and garlands to the gates, and would have done sacrifice with the people.
Sai firist din zafsa wanda dakin yin masa sujada na kofar birni; ya kawo bijimai biyu da furannin da aka saka su kamar gammo; shi da jama'arsa suna so su yi masa hadaya.
14 [Which], when the apostles Barnabas and Paul heard [of], they rent their clothes, and ran in among the people, crying out,
Amma da manzannin, wato Barnaba da Bulus, su ka ji labarin, suka yage rigunansu, suka hanzarta zuwa gun taron mutanen.
15 And saying, Sirs, why do ye these things? We also are men of like passions with you, and preach to you, that ye should turn from these vanities to the living God, who made heaven and earth, and the sea, and all things that are in them.
Suna ta cewa, “Kuji! Ku mutane don me kuke wannan abin? Mu fa mutane ne kamarku. Mun kawo maku labari mai dadi ne, da cewa, ku rabu da abubuwa marar amfani, ku koma ga Allah mai rai, wanda ya hallici sama da kasa da teku da dukan abubuwa da ke cikinsu.
16 Who in times past suffered all nations to walk in their own ways.
A da dai ya bar mutane su yi abinda suka ga dama.
17 Nevertheless he left not himself without witness, in that he did good, and gave us rain from heaven, and fruitful seasons, filling our hearts with food and gladness.
Duk da haka, bai bar kansa ba tare da shaida ba, don yana bada abubuwa masu kyau, yana ba ku ruwan sama, lokatai masu albarka, ya cika ranku da abinci da farin ciki.”
18 And with these sayings they scarce restrained the people from doing sacrifice to them.
Duk da wadannan kalmomin da kyar, Bulus da Barnaba suka iya tsayar da su daga yi masu hadaya.
19 And there came thither [certain] Jews from Antioch, and Iconium, who persuaded the people, and having stoned Paul, drew [him] out of the city, supposing him to be dead.
Amma wasu Yahudawa daga Antakiya da wasunsu daga Ikoniya suka rinjayi tarun jama'ar. Suka jajjefi Bulus suka ja shi zuwa wajen garin, suna ganin kamar ya mutu.
20 But as the disciples stood around him, he rose, and came into the city: and the next day he departed with Barnabas to Derbe.
Duk da haka da almajirai suka kewaye shi a tsaitsaye, sai ya tashi ya koma cikin garin. Washegari, ya tafi Darba tare Barnaba.
21 And when they had preached the gospel to that city, and had taught many, they returned again to Lystra, and [to] Iconium, and to Antioch,
Bayan sun yi wa'azin bishara a wannan birnin suka kuma sami almajirai da yawa, suka dawo Listira, da Ikoniya da Antikiya.
22 Confirming the souls of the disciples, exhorting them to continue in the faith, and that we must through much tribulation enter into the kingdom of God.
Suna karfafa zuciyar almajiran su rike bangaskiyarsu, su ci gaba da ita, suna ce masu, “Ta wurin jimrewa mai yawa zamu shiga mulkin Allah, don haka dole ne mu sha wahala.”
23 And when they had ordained for them elders in every church, and had prayed with fasting, they commended them to the Lord, on whom they believed.
Da suka zabar masu dattawa a kowace iklisiya, sai suka yi addu'oi da azumi, suka mika su ga Ubangiji, ga wanda suka gaskanta a gareshi.
24 And after they had passed throughout Pisidia, they came to Pamphylia.
Sa'annan sun bi ta Bisidiya suka kai Bamfiliya.
25 And when they had preached the word in Perga, they went down into Attalia:
Da suka yi maganarsu a Biriya, sun wuce zuwa har Italiya.
26 And thence sailed to Antioch, from whence they had been commended to the grace of God, for the work which they fulfilled.
Ta jirgin ruwa zuwa Antakiya, a nan ne aka mika su ga alherin Allah don aikin da suka gama a yanzu.
27 And when they had come, and had assembled the church, they rehearsed all that God had done with them, and that he had opened the door of faith to the Gentiles.
Da isowarsu Antakiya sun tara 'yan iklisiya a wuri daya, sun ba da labarin dukan abin da Allah ya yi ta wurinsu. Da yadda Ya bude kofa a wurin al'ummai ta bangaskiya.
28 And there they abode a long time with the disciples.
Sun zauna tare da almajiran na tsawon lokaci.

< Acts 14 >