< Acts 14 >

1 And it came to pass in Iconium, that they went both together into the synagogue of the Jews, and so spoke, that a great multitude both of the Jews, and also of the Greeks, believed.
A Ikoniyum Bulus da Barnabas suka shiga majami’ar Yahudawa yadda suka saba. A can suka yi magana gabagadi har Yahudawa da Al’ummai masu yawa suka gaskata.
2 But the unbelieving Jews stirred up the Gentiles, and made their minds evil-affected against the brethren.
Amma Yahudawan da suka ƙi ba da gaskata, suka zuga Al’ummai suka sa ɓata tsakaninsu da’yan’uwa.
3 A long time therefore they abode speaking boldly in the Lord, who gave testimony to the word of his grace, and granted signs and wonders to be done by their hands.
Bulus da Barnabas kuwa suka daɗe sosai a can, suna magana gabagadi saboda Ubangiji, wanda kuwa ya tabbatar da saƙon alherinsa ta wurinsa su su aikata ayyuka da alamu masu banmamaki.
4 But the multitude of the city was divided: and part held with the Jews, and part with the apostles.
Mutanen birnin suka rarrabu, waɗansu suka goyi bayan Yahudawa, waɗansu kuma suka goyi bayan manzannin.
5 And when there was an assault made both of the Gentiles, and also of the Jews, with their rulers, to use [them] despitefully, and to stone them,
Yahudawa da Al’ummai tare da shugabanninsu suka ƙulla shawara a tsakaninsu, domin su wulaƙanta su su kuma jajjefe su da duwatsu.
6 Being apprised of [it], they fled to Lystra and Derbe, cities of Lycaonia, and to the region in that vicinity.
Amma suka sami labari suka kuma gudu zuwa biranen Ikoniyum na Listira da Derbe da kuma ƙauyukan kewaye,
7 And there they preached the gospel.
inda suka ci gaba da wa’azin labari mai daɗi.
8 And there sat a certain man at Lystra, impotent in his feet, being a cripple from his mother's womb, who had never walked.
A Listira kuwa akwai wani gurgu zaune a ƙafafunsa, wanda gurgu ne tun haihuwa, kuma bai taɓa tafiya ba.
9 The same heard Paul speak: who steadfastly beholding him, and perceiving that he had faith to be healed,
Ya kasa kunne yayinda Bulus yake magana. Bulus kuma ya kafa masa ido, ya lura cewa yana da bangaskiyar da za tă warkar da shi
10 Said with a loud voice, Stand upright on thy feet. And he leaped and walked.
sai ya ɗaga murya ya ce, “Tashi ka tsaya kan ƙafafunka!” Da jin haka, sai mutumin ya yi wuf ya kuma fara tafiya.
11 And when the people saw what Paul had done, they lifted up their voices, saying in the speech of Lycaonia, The gods have come down to us in the likeness of men.
Sa’ad da taron suka ga abin da Bulus ya yi, sai suka ihu da harshen Likayoniyawa, suna cewa, “Alloli sun sauka mana da siffar mutane!”
12 And they called Barnabas, Jupiter, and Paul, Mercurius, because he was the chief speaker.
Sai suka ba wa Barnabas, sunan Zeyus, Bulus kuma suka kira Hermes domin shi ne shugaban magana.
13 Then the priest of Jupiter, who was before their city, brought oxen and garlands to the gates, and would have done sacrifice with the people.
Firist na Zeyus, wanda haikalinsa ke bayan birni, ya kawo bijimai da furanni a ƙofofin birni domin shi da taron mutanen sun so su miƙa musu hadayu.
14 [Which], when the apostles Barnabas and Paul heard [of], they rent their clothes, and ran in among the people, crying out,
Amma da manzannin nan Barnabas da Bulus suka ji haka, sai suka yayyage tufafinsu suka ruga cikin taron, suna ihu suna cewa,
15 And saying, Sirs, why do ye these things? We also are men of like passions with you, and preach to you, that ye should turn from these vanities to the living God, who made heaven and earth, and the sea, and all things that are in them.
“Ya ku mutane, don me kuke yin haka? Ai, mu ma mutane ne kawai,’yan adam ne kamar ku. Mun kawo muku labari mai daɗi ne, muna gaya muku ku juya daga waɗannan abubuwa banza, ku juyo ga Allah mai rai, wanda ya yi sama da ƙasa da teku da kuma dukan abin da yake cikinsu.
16 Who in times past suffered all nations to walk in their own ways.
A zamanin dā, ya bar dukan ƙasashe su yi yadda suka ga dama.
17 Nevertheless he left not himself without witness, in that he did good, and gave us rain from heaven, and fruitful seasons, filling our hearts with food and gladness.
Duk da haka bai bar kansa babu shaida ba. Ya nuna alheri ta wurin ba ku ruwan sama da kuma amfanin gona a lokutansu; ya ba ku abinci mai yawa ya kuma cika zukatanku da farin ciki.”
18 And with these sayings they scarce restrained the people from doing sacrifice to them.
Ko da waɗannan kalmomi ma, da ƙyar suka hana jama’an nan yin musu hadaya.
19 And there came thither [certain] Jews from Antioch, and Iconium, who persuaded the people, and having stoned Paul, drew [him] out of the city, supposing him to be dead.
Sai waɗansu Yahudawa suka zo daga Antiyok da Ikoniyum suka sha kan taron. Suka jajjefi Bulus da duwatsu suka kuma ja shi bayan birni, suna tsammani ya mutu.
20 But as the disciples stood around him, he rose, and came into the city: and the next day he departed with Barnabas to Derbe.
Amma bayan da almajiran suka taru kewaye da shi, sai ya tashi ya koma cikin birni. Kashegari shi da Barnabas suka tashi zuwa Derbe.
21 And when they had preached the gospel to that city, and had taught many, they returned again to Lystra, and [to] Iconium, and to Antioch,
Suka yi wa’azin Labari mai daɗi a wannan birni, suka kuma sami almajirai da yawa. Sai suka koma Listira, Ikoniyum da kuma Antiyok,
22 Confirming the souls of the disciples, exhorting them to continue in the faith, and that we must through much tribulation enter into the kingdom of God.
suna gina almajirai suna kuma ƙarfafa su su tsaya da gaske cikin bangaskiya. Suka ce, “Sai da shan wahaloli masu yawa za mu shiga mulkin Allah.”
23 And when they had ordained for them elders in every church, and had prayed with fasting, they commended them to the Lord, on whom they believed.
Bulus da Barnabas suka naɗa musu dattawa a kowace ikkilisiya, tare da addu’a da azumi, suka miƙa su ga Ubangiji, wanda suka dogara da shi.
24 And after they had passed throughout Pisidia, they came to Pamphylia.
Bayan sun bi ta Fisidiya, sai suka zo cikin Famfiliya,
25 And when they had preached the word in Perga, they went down into Attalia:
kuma sa’ad da suka yi wa’azi a Ferga, sai suka gangara zuwa Attaliya.
26 And thence sailed to Antioch, from whence they had been commended to the grace of God, for the work which they fulfilled.
Daga Attaliya kuma suka shiga jirgin ruwa suka koma Antiyok, inda dā aka danƙa su ga alherin Allah saboda aikin da suka kammala yanzu.
27 And when they had come, and had assembled the church, they rehearsed all that God had done with them, and that he had opened the door of faith to the Gentiles.
Da isarsu a can, sai suka tara ikkilisiya wuri ɗaya suka ba da rahoton duk abin da Allah ya aikata ta wurinsu da kuma yadda ya buɗe ƙofar bangaskiya domin Al’ummai.
28 And there they abode a long time with the disciples.
Suka kuma jima a can tare da almajirai.

< Acts 14 >