< 2 Thessalonians 1 >
1 Paul, and Silvanus, and Timothy, to the church of the Thessalonians in God our Father and the Lord Jesus Christ:
Bulus, da Sila, da Timoti, Zuwa ga ikkilisiya ta Tessalonikawa ta Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi.
2 Grace to you, and peace, from God our Father and the Lord Jesus Christ.
Alheri da salama daga Allah Uba da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
3 We are bound to thank God always for you, brethren, as it is meet, because your faith groweth exceedingly, and the charity of every one of you all towards each other aboundeth;
Dole kullum mu gode wa Allah saboda ku,’yan’uwa, haka kuwa ya dace, domin bangaskiyarku tana girma gaba-gaba, ƙaunar da kowannenku yake yi wa juna kuwa tana ƙaruwa.
4 So that we ourselves glory in you in the churches of God, for your patience and faith in all your persecutions and tribulations that ye endure:
Saboda haka, a cikin ikkilisiyoyin Allah muna taƙama game da daurewarku da kuma bangaskiyarku cikin dukan tsanani da gwaje-gwajen da kuke sha.
5 [Which is] a manifest token of the righteous judgment of God, that ye may be counted worthy of the kingdom of God, for which ye also suffer:
Dukan wannan yana tabbatar cewa hukuncin Allah daidai ne, saboda haka kuma za a lissafta ku a kan kun cancanci mulkin Allah, wanda dominsa ne kuke shan wahala.
6 Seeing [it is] a righteous thing with God to recompense tribulation to them that trouble you;
Allah mai adalci ne, Zai sāka wa masu ba ku wahala da wahala
7 And to you who are troubled, rest with us, when the Lord Jesus shall be revealed from heaven with his mighty angels,
yă kuma sauƙaƙa muku ku da kuke wahala, har ma da mu. Wannan zai faru sa’ad da aka bayyana Ubangiji Yesu daga sama cikin wuta mai ci tare da mala’ikunsa masu iko.
8 In flaming fire taking vengeance on them that know not God, and that obey not the gospel of our Lord Jesus Christ:
Zai hukunta waɗanda ba su san Allah ba da kuma waɗanda ba su yi biyayya da bisharar Ubangijinmu Yesu ba.
9 Who shall be punished with everlasting destruction from the presence of the Lord, and from the glory of his power; (aiōnios )
Za a hukunta su da madawwamiyar hallaka a kuma kau da su daga gaban Ubangiji da kuma daga ɗaukakar ikonsa (aiōnios )
10 When he shall come to be glorified in his saints, and to be admired by all them that believe (because our testimony among you was believed) in that day.
a ranar da zai dawo don a ɗaukaka shi a cikin mutanensa masu tsarki, yă kuma zama abin banmamaki ga dukan waɗanda suka gaskata. Wannan ya haɗa har da ku, domin kun gaskata shaidar da muka yi muku.
11 Wherefore also we pray always for you, that our God would count you worthy of [this] calling, and fulfill all the good pleasure of [his] goodness, and the work of faith with power:
Sane da wannan, kullum muna addu’a saboda ku, don Allahnmu yă sa ku cancanci kiransa, ta wurin ikonsa kuma yă cika kowace manufarku mai kyau da kuma kowane aikin da bangaskiyarku ta iza.
12 That the name of our Lord Jesus Christ may be glorified in you, and ye in him, according to the grace of our God, and of the Lord Jesus Christ.
Muna wannan addu’a don sunan Ubangijinmu Yesu yă sami ɗaukaka a cikinku, ku kuma a cikinsa, bisa ga alherin Allahnmu da na Ubangiji Yesu Kiristi.