< 2 Samuel 22 >
1 And David spoke to the LORD the words of this song in the day [that] the LORD had delivered him from the hand of all his enemies, and from the hand of Saul:
Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
2 And he said, The LORD [is] my rock, and my fortress, and my deliverer;
Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
3 The God of my rock; in him will I trust: [he is] my shield, and the horn of my salvation, my high tower, and my refuge, my preserver; thou savest me from violence.
Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
4 I will call on the LORD, [who is] worthy to be praised: so shall I be saved from my enemies.
“Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
5 When the waves of death compassed me, the floods of ungodly-men made me afraid;
Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
6 The sorrows of hell encompassed me; the snares of death seized me; (Sheol )
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol )
7 In my distress I called upon the LORD, and cried to my God: and he heard my voice out of his temple, and my cry [entered] into his ears.
“A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
8 Then the earth shook and trembled: the foundations of heaven moved and shook, because he was wroth.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
9 There went up a smoke out of his nostrils, and fire out of his mouth devoured: coals were kindled by it.
Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
10 He bowed the heavens also, and came down; and darkness [was] under his feet.
Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
11 And he rode upon a cherub, and flew: and he was seen upon the wings of the wind.
Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
12 And he made darkness pavilions around him, dark waters, [and] thick clouds of the skies.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
13 Through the brightness before him were coals of fire kindled.
Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
14 The LORD thundered from heaven, and the most High uttered his voice.
Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
15 And he sent out arrows, and scattered them; lightning, and discomfited them.
Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
16 And the channels of the sea appeared, the foundations of the world were laid open, at the rebuking of the LORD, at the blast of the breath of his nostrils.
Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
17 He sent from above, he took me; he drew me out of many waters;
“Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
18 He delivered me from my strong enemy, from them that hated me: for they were too strong for me.
Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
19 They fell upon me in the day of my calamity: but the LORD was my support.
Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
20 He brought me forth also into a large place: he delivered me, because he delighted in me.
Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
21 The LORD rewarded me according to my righteousness: according to the cleanness of my hands hath he recompensed me.
“Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
22 For I have kept the ways of the LORD, and have not wickedly departed from my God.
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
23 For all his judgments [were] before me: and [as for] his statutes, I did not depart from them.
Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
24 I was also upright before him, and have kept myself from my iniquity.
Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
25 Therefore the LORD hath recompensed me according to my righteousness; according to my cleanness in his eye-sight.
Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
26 With the merciful thou wilt show thyself merciful, [and] with the upright man thou wilt show thyself upright.
“Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
27 With the pure thou wilt show thyself pure; and with the froward thou wilt contend.
ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
28 And the afflicted people thou wilt save: but thy eyes [are] upon the haughty, [that] thou mayest bring [them] down.
Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
29 For thou [art] my lamp, O LORD: and the LORD will lighten my darkness.
Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
30 For by thee I have run through a troop: by my God have I leaped over a wall.
Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
31 [As for] God, his way [is] perfect; the word of the LORD [is] tried: he [is] a buckler to all them that trust in him.
“Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
32 For who [is] God, save the LORD? and who [is] a rock, save our God?
Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
33 God [is] my strength [and] power: and he maketh my way perfect.
Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
34 He maketh my feet like hinds' [feet]: and setteth me upon my high places.
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
35 He teacheth my hands to war; so that a bow of steel is broken by my arms.
Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
36 Thou hast also given me the shield of thy salvation: and thy gentleness hath made me great.
Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
37 Thou hast enlarged my steps under me; so that my feet have not slipped.
Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
38 I have pursued my enemies, and destroyed them; and turned not again until I had consumed them.
“Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
39 And I have consumed them, and wounded them, that they could not arise: yea, they have fallen under my feet.
Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
40 For thou hast girded me with strength to battle: them that rose up against me hast thou subdued under me.
Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
41 Thou hast also given me the necks of my enemies, that I might destroy them that hate me.
Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
42 They looked, but [there was] none to save; [even] to the LORD, but he answered them not.
Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
43 Then I beat them as small as the dust of the earth, I stamped them as the mire of the street, [and] spread them abroad.
Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
44 Thou also hast delivered me from the strivings of my people, thou hast kept me [to be] head of the heathen: a people [which] I knew not shall serve me.
“Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
45 Strangers shall submit themselves to me: as soon as they hear, they shall be obedient to me.
baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
46 Strangers shall fade away, and they shall tremble from their close places.
Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
47 The LORD liveth; and blessed [be] my rock; and exalted be the God of the rock of my salvation.
“Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
48 It [is] God that avengeth me, and that bringeth down the people under me,
Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
49 And that bringeth me forth from my enemies: thou also hast lifted me up on high above them that rose up against me: thou hast delivered me from the violent man.
wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
50 Therefore I will give thanks to thee, O LORD, among the heathen, and I will sing praises to thy name.
Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
51 [He is] the tower of salvation for his king: and [he] showeth mercy to his anointed, to David, and to his seed for evermore.
“Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”