< 2 John 1 >
1 The elder to the elect lady, and her children, whom I love in the truth; and not I only, but also all they that have known the truth;
Daga dattijon zuwa ga uwar gida zababbiya da yayanta, wadanda nake kauna da gaskiya, ba ni kadai ba, amma da dukan wadanda sun san gaskiya -
2 For the truth's sake which dwelleth in us, and shall be with us for ever. (aiōn )
domin gaskiya da take cikinmu za ta kuma kasance tare da mu har abada. (aiōn )
3 Grace be with you, mercy, [and] peace from God the Father, and from the Lord Jesus Christ, the Son of the Father, in truth and love.
Alheri da jinkai da salama za su kasance tare da mu, daga Allah Uba da kuma daga Yesu Almasihu Dan Uba, a cikin gaskiya da kauna.
4 I rejoiced greatly, that I found of thy children walking in truth, as we have received a commandment from the Father.
Na yi murna sosai sa'anda na sami wadansu yayanki suna tafiya cikin gaskiya, kamar yadda muka karbi wannan umarni daga Uba.
5 And now I beseech thee, lady, not as though I wrote a new commandment to thee, but that which we had from the beginning, that we love one another.
Yanzu ina rokon ki, uwar gida, ba kamar ina rubuta maki sabon umarni ba, amma wannan da muka samu tun da can, cewa mu kaunaci junanmu.
6 And this is love, that we walk according to his commandments. This is the commandment, that as ye have heard from the beginning, ye should walk in it.
Wannan kuma itace kauna, cewa mu yi tafiya bisa ga umarnin sa. Wannan shine umarnin, daidai kamar yadda kuka ji da fari, da cewa ku yi tafiya a cikinsa.
7 For many deceivers have entered into the world, who confess not that Jesus Christ is come in the flesh. This is a deceiver, and an antichrist.
Gama masu yaudara sun fito a duniya, wadanda ba su yarda cewa Yesu ya zo cikin jiki ba. Wannan ne mayaudari da kuma magabcin Almasihu.
8 Look to yourselves, that we lose not those things which we have wrought, but that we receive a full reward.
Ku dubi kanku, domin kada ku rasa abubuwan da mu duka muka yi aiki a kansu, amma domin ku karba dukan sakamon ku.
9 Whoever transgresseth, and abideth not in the doctrine of Christ, hath not God. He that abideth in the doctrine of Christ, he hath both the Father and the Son.
Duk wanda ya ci gaba da tafiya ba cikin koyarwa Almasihu ba, ba shi da Allah. Wanda ya zauna cikin koyarwar kwa yana tare da Uban da kuma Dan.
10 If any one cometh to you, and bringeth not this doctrine, receive him not into [your] house, neither wish him happiness:
Duk wanda ya zo wurinku, ba tare da wannan koyarwar ba, kar ku karbe shi cikin gidanku, kada ma ku gaishe shi.
11 For he that wisheth him happiness, is partaker of his evil deeds.
Domin duk wanda ya gaishe shi ya yi tarayya da shi kenan cikin miyagun ayyukan sa.
12 Having many things to write to you, I would not [write] with paper and ink: but I trust to come to you, and speak face to face, that our joy may be full.
Ina da abubuwa dayawa da nake so in rubuta maki amma al'kalami tawada da takarda baza su iya daukar su duka ba. Amma duk da haka ina begen zuwa gare ki domin mu yi magana fuska da fuska, domin farin cikn mu ya zama cikakke.
13 The children of thy elect sister greet thee. Amen.
Yayan yar'uwarki zababbiya suna gaishe ki.