< 2 Corinthians 2 >

1 But I determined this with myself, that I would not come again to you in heaviness.
Saboda haka na yanke shawara ba zan sāke kawo muku ziyara ta ɓacin rai ba.
2 For if I make you sorry, who is he then that maketh me glad, but the same who is made sorry by me?
Gama in na sa ku baƙin ciki, wa ya rage yă faranta mini zuciya, in ba ku waɗanda na sa baƙin cikin ba?
3 And I wrote this same to you, lest, coming I should have sorrow from them by whom I ought to rejoice; having confidence in you all, that my joy is [the joy] of you all.
Na rubuta yadda na yi ne saboda sa’ad da na iso kada waɗanda ya kamata su faranta mini rai, su sa ni baƙin ciki. Na amince da ku duka a kan farin cikina naku ne ku duka.
4 For out of much affliction and anguish of heart I wrote to you with many tears; not that ye should be grieved, but that ye might know the love which I have more abundantly to you.
Gama na rubuta muku ne cikin baƙin ciki mai yawa da ɓacin zuciya har ma da hawaye mai yawa, ba don in sa ku baƙin ciki ba ne, a’a, sai dai domin in nuna muku zurfin ƙaunar da nake yi muku.
5 But if any hath caused grief, he hath not grieved me, but in part: that I may not overcharge you all.
In wani ya jawo baƙin ciki, ba ni kaɗai ya jawo wa ba, amma a wani fanni, sai in ce dukanku ne ya jawo wa, ba na faɗa haka don in matsa muku lamba ba ne.
6 Sufficient to such a man [is] this punishment, which [was inflicted] by many.
Irin wannan mutum, horon da yawancin mutane suka yi masa ya isa haka.
7 So that on the other hand, ye [ought] rather to forgive [him], and comfort [him], lest perhaps such one should be swallowed up with excessive sorrow.
Yanzu fa, a maimako, gara ku yafe masa, ku kuma ta’azantar da shi, don kada baƙin ciki mai yawa yă sha kansa.
8 Wherefore I beseech you that ye would confirm [your] love towards him.
Saboda haka, ina roƙonku, ku sāke nuna masa ƙaunarku.
9 For to this end also I wrote, that I might know the proof of you, whether ye are obedient in all things.
Abin da ya sa na rubuta muku shi ne don in ga ko za ku jimre da gwajin nan, kuna kuma yin biyayya ta kowace hanya.
10 To whom ye forgive any thing, I [forgive] also: for if I forgave any thing, to whom I forgave [it], for your sakes [I forgave it], in the person of Christ;
In kuka gafarta wa wani, ni ma na gafarta masa. Abin da na gafarta kuwa, in har ma da abin gafartawa, saboda ku ne na gafarta masa, albarkacin Kiristi,
11 Lest Satan should get an advantage of us: for we are not ignorant of his devices.
don kada Shaiɗan yă rinjaye mu. Da yake muna sane da dabarunsa.
12 Furthermore, when I came to Troas to [preach] the gospel of Christ, and a door was opened to me by the Lord,
To, sa’ad da na tafi Toruwas don in yi wa’azin bisharar Kiristi, ko da yake na tarar cewa Ubangiji ya buɗe mini ƙofa,
13 I had no rest in my spirit, because I found not Titus my brother; but taking my leave of them, I went from thence into Macedonia.
duk da haka, ban sami salama a zuciyata ba domin ban sami ɗan’uwana Titus a can ba. Sai na yi bankwana da su na wuce zuwa Makidoniya.
14 Now thanks [be] to God, who always causeth us to triumph in Christ, and maketh manifest the savor of his knowledge by us in every place.
Amma godiya ga Allah, wanda kullum yake bi da mu da nasara cikin Kiristi, kuma ta wurinmu, yana baza ƙanshin nan na sanin Kiristi a ko’ina.
15 For we are to God a sweet savor of Christ, in them that are saved, and in them that perish:
Don kuwa, a wurin Allah mu ƙanshin Kiristi ne cikin waɗanda ake ceto, da kuma waɗanda suke hanyar hallaka.
16 To the one [we are] the savor of death to death; and to the other the savor of life to life. And who [is] sufficient for these things?
Ga wani, mu warin mutuwa ne, amma ga wani kuwa, mu ƙanshin rai ne. Wa ya isa yă yi irin wannan aikin?
17 For we are not as many, who corrupt the word of God: but as from sincerity, but as from God, in the sight of God we speak in Christ.
Ba ma tallar maganar Allah don riba yadda waɗansu mutane da yawa suke yi. A maimakon haka, muna magana cikin Kiristi a gaban Allah da gaskiya, kamar mutanen da aka aika daga Allah.

< 2 Corinthians 2 >