< 1 Timothy 6 >

1 Let as many servants as are under the yoke count their own masters worthy of all honor, that the name of God and [his] doctrine may not be blasphemed.
Bari duk wadanda ke bayi a karkashin karkiya su ga iyayengijinsu sun cancanci dukan daraja. Su yi haka domin kada a sabawa sunan Allah da koyarwarsa.
2 And they that have believing masters, let them not despise [them], because they are brethren; but rather do [them] service, because they are faithful and beloved, partakers of the benefit. These things teach and exhort.
Bayin da suke da iyayengiji da ke masu ba da gaskiya kada su rena su saboda su 'yan'uwa ne. A maimakon haka, su yi masu hidima da kwazo. Gama iyayengijin da suke cin ribar aikinsu masu bi ne, kaunattatu kuma. Ka koyar ka kuma bayyana wadannan abubuwa.
3 If any man teacheth otherwise, and consenteth not to wholesome words, [even] the words of our Lord Jesus Christ, and the doctrine which is according to godliness,
Idan ya kasance wani na koyar da wani abu dabam bai kuma yarda da amintaciyar koyarwa ba, wato maganar Ubangijinmu Yesu Almasihu. Alal misali ba su amince da koyarwa da ke kai ga Allahntaka ba.
4 He is proud, knowing nothing, but doting about questions and strifes of words, from which cometh envy, strife, railings, evil surmisings,
Wannan mutum mai girman kai ne, kuma bai san komai ba. A maimakon haka, yana da matukar jayayya da gardama game da kalmomi. Wadannan kalmomi na kawo kishi, da husuma, da zage-zage, da miyagun zace-zace, da
5 Perverse disputings of men of corrupt minds, and destitute of the truth, supposing gain to be godliness: from such withdraw thyself.
yawan rashin jituwa tsakanin mutane masu rubabbun hankula. Sun bijire wa gaskiya. Suna tunani cewa ibada hanya ce ta yin arziki.” Ka zame daga wadannan abubuwa.
6 But godliness with contentment is great gain.
Yanzu bin Allah tare da dangana babbar riba ce.
7 For we brought nothing into [this] world, [and it is] certain we can carry nothing out.
Gama ba mu kawo komai a duniya ba, ba zamu iya fita cikinta da komai ba.
8 And having food and raiment, with these let us be content.
A maimakon haka, mu dangana da abinci da kuma sutura.
9 But they that will be rich, fall into temptation, and a snare, and [into] many foolish and hurtful lusts, which drown men in destruction and perdition.
To wadanda ke son zama mawadata su kan fada cikin jaraba, cikin tarko. Suna fadawa cikin abubuwan wauta da sha'awoyi masu illa da kowanne abu da ke sa mutane su dulmaya cikin lallacewa da hallaka.
10 For the love of money is the root of all evil: which while some have coveted, they have erred from the faith, and pierced themselves through with many sorrows.
Gama son kudi shine tushen kowacce irin mugunta. Wadansu mutane garin neman kudi sun kauce daga bangaskiya, sun kuma jawowa kansu bakin ciki mai yawa.
11 But thou, O man of God, flee from these things; and follow after righteousness, godliness, faith, love, patience, meekness.
Amma kai, mutumin Allah, ka guji wadannan abubuwa, ka bi adalci, ibada, aminci, kauna, jimiri, da tawali'u.
12 Fight the good fight of faith, lay hold on eternal life, to which thou art also called, and hast professed a good profession before many witnesses. (aiōnios g166)
Ka yi fama, fama mai kyau na bangaskiya. Ka kama rai madawami da aka kira ka gare shi. A kan wannan ne ka ba da shaida a gaban shaidu masu yawa game da abin da ke da kyau. (aiōnios g166)
13 I give thee charge in the sight of God, who maketh alive all things, and [before] Christ Jesus, who before Pontius Pilate testified a good confession;
Ina ba ka wannan umarni a gaban Allah wanda ke rayar da dukan abubuwa, da gaban Almasihu Yesu, wanda ya fadi abin da ke gaskiya ga Bilatus Babunti.
14 That thou keep [this] commandment without spot, unrebukable, until the appearing of our Lord Jesus Christ:
Ka bi doka daidai, babu abin zargi har bayanuwar Ubangijinmu Yesu Almasihu.
15 Which in his times he will show [who is] the blessed and only Potentate, the King of kings, and Lord of lords;
Allah zai nuna bayyanuwarsa a daidai lokaci- Allah, mai albarka, Makadaicin iko, Sarkin da ke sarauta, Ubangiji mai mulki.
16 Who only hath immortality, dwelling in the light which no man can approach; whom no man hath seen, nor can see: to whom [be] honor and power everlasting. Amen. (aiōnios g166)
Shine kadai marar mutuwa, mai zama cikin hasken da ba ya kusantuwa. Ba wanda ke ganinsa, ko ya iya hango shi. Girma ya tabbata a gare shi da kuma madawwamin iko. Amin. (aiōnios g166)
17 Charge them that are rich in this world, that they be not high-minded, nor trust in uncertain riches, but in the living God, who giveth us richly all things to enjoy; (aiōn g165)
Ka gaya wa masu dukiya a cikin wannan duniya kada su daga kai, kada su sa bege ga arziki mara dawwama. Maimamakon haka, su sa begensu ga Allah wanda ke ba mu wadatar gaske domin jin dadin mu. (aiōn g165)
18 That they do good, that they be rich in good works, ready to distribute, willing to communicate;
Gaya masu su yi nagarta su arzurta a ayyuka nagari, su zama masu bayarwa hannu sake.
19 Laying up in store for themselves a good foundation against the time to come, that they may lay hold on eternal life.
Ta haka za su ajiye wa kansu harsashi mai kyau kan abin da ke zuwa domin su amshi rayuwa ta kwarai.
20 O Timothy, keep that which is committed to thy trust, avoiding profane [and] vain babblings, and oppositions of science falsely so called;
Timoti, ka kare abin da aka ba ka. Ka nisanci maganar wauta da gardamomin da ke sabawa juna wanda ake kira ilimi a karyace.
21 Which some professing, have erred concerning the faith. Grace [be] with thee. Amen.
Wadansu mutane suna shelar wadannan abubuwa, don haka sun kauce wa bangaskiyar. Bari alheri ya kasance tare da kai.

< 1 Timothy 6 >