< 1 Samuel 29 >

1 Now the Philistines collected all their armies to Aphek: and the Israelites encamped by a fountain which [is] in Jezreel.
Filistiyawa suka tattara dukan rundunoninsu a Afek. Isra’ila kuwa suka yi sansani kusa da maɓulɓular da take Yezireyel.
2 And the lords of the Philistines passed on by hundreds, and by thousands: but David and his men passed on in the rear with Achish.
Sa’ad da sarakuna Filistiyawa suke wucewa da rundunarsu na mutum ɗari-ɗari da na dubu-dubu. Dawuda da mutanensa suna biye a baya tare da Akish.
3 Then said the princes of the Philistines, What [do] these Hebrews [here]? And Achish said to the princes of the Philistines, [Is] not this David, the servant of Saul the king of Israel, who hath been with me these days, or these years, and I have found no fault in him since he fell [to me] to this day?
Komandodin Filistiyawa suka ce, “Waɗannan Ibraniyawa kuma fa?” Akish ya ce, “Wannan shi ne Dawuda hafsan Shawulu, sarkin Isra’ila. Yana nan tare da ni shekara guda ke nan. Ban kuwa taɓa samunsa da wani lahani ba tun daga ranar da ya bar Shawulu.”
4 And the princes of the Philistines were wroth with him; and the princes of the Philistines said to him, Make this man return, that he may go again to his place which thou hast appointed him, and let him not go down with us to battle, lest in the battle he should be an adversary to us: for with what would he reconcile himself to his master? [would it] not [be] with the heads of these men?
Amma komandodin Filistiyawa suka yi fushi, suka ce, “Ka sa mutumin nan yă koma zuwa wurin da ka ba shi yă zauna. Ba zai bi mu zuwa wurin yaƙi ba. Yana iya juya a kanmu lokacin yaƙin. Zai iya yin amfani da wannan zarafi yă ciccire kawunanmu don yă faranta wa maigidansa rai?
5 [Is] not this David, of whom they sung one to another in dances, saying, Saul slew his thousands, and David his ten thousands?
Tuna fa, ba shi ne Dawuda ɗin da ake girmama da rawa da waƙoƙi ana cewa, “‘Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa dubbun dubbai ba’?”
6 Then Achish called David, and said to him, Surely, [as] the LORD liveth, thou hast been upright, and thy going out and thy coming in with me in the host [is] good in my sight: for I have not found evil in thee from the day of thy coming to me to this day: nevertheless the lords favor thee not.
Saboda haka Akish ya kira Dawuda ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, na amince da kai tun daga ranar da ka zo wurina har yă zuwa yau, ban same ka da wani laifi ba, na kuma yi farin ciki in sa ka a cikin sojojina don ka yi mini aiki. Amma masu mulki nawa ba su yarda da kai ba.
7 Therefore now return, and go in peace, that thou displease not the lords of the Philistines.
Sai ka juya ka koma ka isa lafiya ba tare da ɓata wa masu mulkin Filistiyawa rai ba.”
8 And David said to Achish, But what have I done? and what hast thou found in thy servant, so long as I have been with thee to this day, that I may not go and fight against the enemies of my lord the king.
Dawuda ya ce wa Akish, “Me na yi? Ka taɓa samun bawanka da laifi tun daga ranar da na zo har zuwa yanzu? Ina dalilin da ba zan tafi tare da kai in yaƙi maƙiyin ranka yă daɗe, sarki ba?”
9 And Achish answered and said to David, I know that thou [art] good in my sight, as an angel of God: notwithstanding, the princes of the Philistines have said, He shall not go up with us to the battle.
Akish ya ce, “A ganina kai marar laifi ne kamar mala’ikan Allah, duk da haka shugabannin sojojin Filistiyawa sun ce, ‘Ba zai tafi yaƙi tare da mu ba.’
10 Wherefore now rise early in the morning with thy master's servants that are come with thee: and as soon as ye shall have risen early in the morning, and have light, depart.
Ka tashi da sassafe, kai da bayin shugabanka da suka zo tare da kai. Da gari ya waye sai ku kama hanya.”
11 So David and his men rose early to depart in the morning, to return into the land of the Philistines. And the Philistines went up to Jezreel.
Gari na wayewa tun da sassafe Dawuda da mutanensa suka tashi suka kama hanyar komawa ƙasar Filistiyawa. Filistiyawa kuwa suka haura zuwa Yezireyel.

< 1 Samuel 29 >