< 1 Samuel 23 >

1 Then they told David, saying, Behold, the Philistines fight against Keilah, and they rob the threshing-floors.
Sa’ad da aka ce wa Dawuda, “Duba ga Filistiyawa suna yaƙi da mutanen Keyila, suna kwashe musu hatsi a masussukai.”
2 Therefore David inquired of the LORD, saying, Shall I go and smite these Philistines? And the LORD said to David, Go, and smite the Philistines, and save Keilah.
Sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya ce, “In tafi in fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi?” Ubangiji kuwa ya ce masa, “Jeka ka yi yaƙi da Filistiyawa, ka ceci Keyila.”
3 And David's men said to him, Behold, we are afraid here in Judah: how much more then if we come to Keilah against the armies of the Philistines?
Amma mutanen Dawuda suka ce masa, “Ga shi, a nan ma a Yahuda muna jin tsoro, balle mu tafi Keyila mu yi yaƙi da sojojin Filistiyawa!”
4 Then David inquired of the LORD yet again. And the LORD answered him and said, Arise, go down to Keilah; for I will deliver the Philistines into thy hand.
Dawuda ya sāke nemi nufin Ubangiji, sai Ubangiji ya ce masa, “Tashi ka gangara zuwa Keyila, gama zan ba da Filistiyawa a hannunka.”
5 So David and his men went to Keilah, and fought with the Philistines, and brought away their cattle, and smote them with a great slaughter. So David saved the inhabitants of Keilah.
Sa’an nan Dawuda da mutanensa suka tafi Keyila, suka yi yaƙi da Filistiyawa, suka kwashe musu shanunsu, suka jijji wa Filistiyawa ƙwarai, suka cece mutanen Keyila daga hannunsu.
6 And it came to pass, when Abiathar the son of Ahimelech fled to David to Keilah, [that] he came down [with] an ephod in his hand.
(Abiyatar ɗan Ahimelek ya zo da efod sa’ad da ya gudo zuwa wurin Dawuda a Keyila.)
7 And it was told to Saul that David had come to Keilah. And Saul said, God hath delivered him into my hand; for he is shut in, by entering into a town that hath gates and bars.
Shawulu ya sami labari cewa Dawuda ya tafi Keyila, sai ya ce, “Allah ya bashe shi a hannuna, domin Dawuda ya kulle kansa ke nan da ya shiga birnin da yake da ƙofofin da ake kulle da ƙarafa.”
8 And Saul called all the people together to war, to go down to Keilah, to besiege David and his men.
Shawulu ya kira dukan sojojinsa don yaƙi, su gangaro zuwa Keyila su mamaye Dawuda da mutanensa.
9 And David knew that Saul secretly plotted mischief against him; and he said to Abiathar the priest, Bring hither the ephod.
Da Dawuda ya ji labari Shawulu yana shirya hanyar da zai kashe shi, sai ya ce wa Abiyatar firist, “Kawo mini efod a nan.”
10 Then said David, O LORD God of Israel, thy servant hath certainly heard that Saul seeketh to come to Keilah, to destroy the city for my sake.
Dawuda ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bawanka ya sami labari cewa tabbatacce Shawulu yana shirin zuwa Keyila yă hallaka garin saboda ni.
11 Will the men of Keilah deliver me up into his hand? will Saul come down as thy servant hath heard? O LORD God of Israel, I beseech thee, tell thy servant. And the LORD said, He will come down.
Mutanen Keyila za su bashe ni a gare shi? Shawulu zai gangaro nan kamar yadda bawanka ya sami labari? Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka gaya wa bawanka.” Ubangiji ya ce, “Zai zo.”
12 Then said David, Will the men of Keilah deliver me and my men into the hand of Saul? And the LORD said, They will deliver [thee] up.
Dawuda ya sāke cewa, “Mutanen Keyila za su bashe ni da mutanena ga Shawulu?” Ubangiji ya ce, “Za su yi.”
13 Then David and his men [who were] about six hundred, arose and departed from Keilah, and went whithersoever they could go. And it was told Saul that David had escaped from Keilah: and he forbore to go forth.
Saboda haka Dawuda da mutanensa wajen mutum ɗari shida suka bar Keyila, suka yi ta tafiya daga wannan wuri zuwa wancan. Sa’ad da aka gaya wa Shawulu cewa Dawuda ya tsere daga Keyila, sai ya fasa tafiya can.
14 And David abode in the wilderness in strong holds, and remained in a mountain in the wilderness of Ziph. And Saul sought him every day, but God delivered him not into his hand.
Dawuda ya zauna a jeji cikin kogunan duwatsu da kuma tuddan jejin Zif. Kowace rana Shawulu ya yi ta neman Dawuda amma Allah bai bashe Dawuda a hannunsa ba.
15 And David saw that Saul had come out to seek his life: and David [was] in the wilderness of Ziph in a wood.
A lokacin da Dawuda yana zaune a Horesh cikin jejin Zif, ya sami labari cewa Shawulu ya fito don yă kashe shi.
16 And Jonathan Saul's son arose, and went to David into the wood, and strengthened his hand in God.
Yonatan ɗan Shawulu kuwa ya tafi wurin Dawuda a Horesh, ya ƙarfafa shi yă dogara ga Allah.
17 And he said to him, Fear not: for the hand of Saul my father shall not find thee; and thou wilt be king over Israel, and I shall be next to thee; and that also Saul my father knoweth.
Ya ce, “Kada ka ji tsoro, mahaifina Shawulu ba zai taɓa sa hannu a kanka ba. Za ka zama sarki a Isra’ila, ni kuma in zama na biyu gare ka. Kai, ko mahaifina Shawulu ma ya san da haka.”
18 And they two made a covenant before the LORD: and David abode in the wood, and Jonathan went to his house.
Su biyunsu kuwa suka ɗaura yarjejjeniya a gaban Ubangiji. Sai Yonatan ya koma gida amma Dawuda ya zauna Horesh.
19 Then came up the Ziphites to Saul to Gibeah, saying, Doth not David hide himself with us in strong holds in the wood, in the hill of Hachilah, which [is] on the south of Jeshimon?
Zifawa suka tafi wurin Shawulu a Gibeya suka ce masa, “Ashe, ba Dawuda ne yake ɓuya a cikinmu a kogwannin duwatsu a Horesh a bisan tudun Hakila, kudu da Yeshimon ba?
20 Now therefore, O king, come down according to all the desire of thy soul to come down; and our part [shall be] to deliver him into the king's hand.
Yanzu, ya sarki, ka gangaro, ka zo a duk lokacin da ka ga ya yi maka, ka zo mu kuma hakkinmu ne mu bashe shi a hannun sarki.”
21 And Saul said, Blessed [be] ye of the LORD; for ye have compassion on me.
Shawulu ya ce, “Ubangiji ya yi muku albarka, gama kun damu da ni.
22 Go, I pray you, prepare yet, and know, and see his place where his haunt is, [and] who hath seen him there: for it is told to me [that] he dealeth very subtilly.
Ku tafi ku ƙara shiri. Ku san inda yakan tafi, wane ne kuma ya gan shi a can. An gaya mini cewa shi mai wayo ne sosai.
23 See therefore, and take knowledge of all the lurking-places where he hideth himself, and come ye again to me with the certainty, and I will go with you: and it shall come to pass, if he is in the land, that I will search him out throughout all the thousands of Judah.
Ku binciko duk wuraren da yakan ɓuya, sai ku dawo ku gaya mini tabbataccen labari. Sa’an nan zan tafi tare da ku in yana can. Zan nemi shi ko’ina cikin dukan kabilar Yahuda.”
24 And they arose, and went to Ziph before Saul: but David and his men [were] in the wilderness of Maon, in the plain on the south of Jeshimon.
Sai suka tashi suka koma Zif, suka sha gaban Shawulu. Dawuda da mutanensa kuwa suna jejin Mawon cikin Araba, kudu da Yeshimon.
25 Saul also and his men went to seek [him]. And they told David: wherefore he came down into a rock, and abode in the wilderness of Maon. And when Saul heard [that], he pursued after David in the wilderness of Maon.
Shawulu da mutanensa suka tafi neman Dawuda. Da Dawuda ya ji labari, sai ya gangara cikin duwatsu ya zauna a cikin jejin Mawon. Sa’ad da Shawulu ya ji haka, sai ya tafi jejin Mawon yana fafaran Dawuda.
26 And Saul went on this side of the mountain, and David and his men on that side of the mountain: and David made haste to get away for fear of Saul; for Saul and his men compassed David and his men around to take them.
Shawulu yana tafiya a gefe ɗaya na dutsen, Dawuda da mutanensa kuma suna a wancan gefe, suna hanzari su ɓace wa Shawulu. Sa’ad da Shawulu da sojojinsa suka kusa cimma Dawuda da mutanensa don su kama su,
27 But there came a messenger to Saul, saying, Haste thee, and come; for the Philistines have invaded the land.
sai wani manzo ya zo wurin Shawulu yana cewa, “Ka koma da sauri, Filistiyawa sun kawo wa ƙasar hari.”
28 Wherefore Saul returned from pursuing after David, and went against the Philistines: therefore they called that place Sela-hammah-lekoth.
Shawulu kuwa ya janye daga fafaran Dawuda, ya tafi yă ƙara da Filistiyawa. Dalilin ke nan da ake kiran wannan wuri Sela Hammalekot, wato, dutsen tserewa.
29 Then David went up from thence, and dwelt in strong holds at En-gedi.
Dawuda kuwa ya haura daga can ya zauna a kogwannin duwatsun En Gedi.

< 1 Samuel 23 >