< 1 Samuel 18 >
1 And it came to pass, when he had made an end of speaking to Saul, that the soul of Jonathan was knit with the soul of David, and Jonathan loved him as his own soul.
Bayan da Dawuda ya gama magana da Shawulu, sai Yonatan ɗan Shawulu ya ji zuciyarsa tana son Dawuda sosai. Yonatan kuwa yana ƙaunar Dawuda kamar ransa.
2 And Saul took him that day, and would let him go no more home to his father's house.
Tun daga wannan rana Shawulu ya zaunar da Dawuda tare da shi, bai bar shi ya koma gidan mahaifinsa ba.
3 Then Jonathan and David made a covenant, because he loved him as his own soul.
Yonatan kuma ya yi yarjejjeniya da Dawuda saboda yana ƙaunarsa kamar ransa.
4 And Jonathan stripped himself of the robe that [was] upon him, and gave it to David, and his garments, even to his sword, and to his bow, and to his girdle.
Yonatan ya tuɓe doguwar taguwarsa da ya sa, ya ba wa Dawuda, tare da sulkensa, har ma da māshi da kibiyarsa, da kuma bel nasa.
5 And David went out whithersoever Saul sent him, [and] behaved himself wisely: and Saul set him over the men of war, and he was accepted in the sight of all the people, and also in the sight of Saul's servants.
Duk abin da Shawulu ya aiki Dawuda yă yi yakan yi shi cikin aminci, har Shawulu ya ba shi babban makami a rundunarsa. Wannan ya faranta wa dukan mutane zuciya har ma da ma’aikatan Shawulu.
6 And it came to pass as they came, when David had returned from the slaughter of the Philistine, that the women came out of all the cities of Israel, singing and dancing, to meet king Saul, with tabrets, with joy, and with instruments of music.
Yayinda mutane suke dawowa gida bayan da Dawuda ya kashe Bafilistin, mata suka fito daga dukan biranen Isra’ila don su sadu da Sarki Shawulu, suna waƙoƙi da raye-raye masu farin ciki, da ganguna da sarewa.
7 And the women answered [one another] as they played, and said, Saul hath slain his thousands, and David his ten thousands.
Suna rawa suna cewa, “Shawulu ya kashe dubbansa, Dawuda kuwa ya kashe dubun dubbai.”
8 And Saul was very wroth, and the saying displeased him; and he said, They have ascribed to David ten thousands, and to me they have ascribed thousands; and [what] can he have more but the kingdom?
Shawulu kuwa ya ji fushi, wannan magana ba tă yi masa daɗi ba, ya yi tunani ya ce, “Suna yabon Dawuda cewa ya kashe dubun dubbai amma ni dubbai kawai. Me ya rage masa yanzu, in ba mulki ba?”
9 And Saul eyed David from that day and forward.
Tun daga wannan lokaci zuwa gaba, Shawulu ya dinga kishin Dawuda.
10 And it came to pass on the morrow, that the evil spirit from God came upon Saul, and he prophesied in the midst of the house: and David played with his hand, as at other times: and [there was] a javelin in Saul's hand.
Kashegari, mugun ruhu daga Allah ya fāɗo wa Shawulu da tsanani. Yana annabci a gidansa, Dawuda kuwa yana bugan molo kamar yadda ya saba. Shawulu yana riƙe da māshi a hannunsa.
11 And Saul cast the javelin; for he said, I will smite David even to the wall. And David escaped from his presence twice.
Da ƙarfi yana magana da kansa yana cewa, “Zan kafe Dawuda da bango.” Amma Dawuda ya bauɗe masa sau biyu.
12 And Saul was afraid of David, because the LORD was with him, and had departed from Saul.
Shawulu ya ji tsoron Dawuda don Ubangiji yana tare da shi, amma Ubangiji ya riga ya bar Shawulu.
13 Therefore Saul removed him from him, and made him his captain over a thousand; and he went out and came in before the people.
Saboda haka Shawulu bai yarda Dawuda yă zauna tare da shi ba, amma ya maishe shi shugaban sojoji dubu. Dawuda kuwa ya riƙa bi da su yana kaiwa yana kuma da tare da su.
14 And David behaved himself wisely in all his ways; and the LORD [was] with him.
A kome da Dawuda ya yi yakan yi nasara gama Ubangiji yana tare da shi.
15 Wherefore when Saul saw that he behaved himself very wisely, he was afraid of him.
Da Shawulu ya ga yadda yake cin nasara, sai ya ji tsoronsa.
16 But all Israel and Judah loved David, because he went out and came in before them.
Amma dukan Isra’ila da Yahuda suka ƙaunaci Dawuda gama yana bin da su a yaƙe-yaƙensu.
17 And Saul said to David, Behold, my elder daughter Merab, her will I give thee for a wife: only be thou valiant for me, and fight the LORD'S battles. For Saul said, Let not my hand be upon him, but let the hand of the Philistines be upon him.
Shawulu ya ce wa Dawuda, “Ga diyata Merab zan ba ka ka aura, kai dai ka yi mini aiki da himma, ka kuma yi yaƙe-yaƙen Ubangiji.” Saboda Shawulu ya ce wa kansa, “Ba zan ɗaga hannuna a kansa ba, Filistiyawa ne za su yi wannan.”
18 And David said to Saul, Who [am] I? and what [is] my life, [or] my father's family in Israel, that I should be son-in-law to the king?
Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Wane ni, wa ya san iyayena ko kabilar iyayena a Isra’ila da zan zama surukin sarki?”
19 But it came to pass at the time when Merab Saul's daughter should have been given to David, that she was given to Adriel the Meholathite to wife.
Da lokaci ya kai da Merab’yar Shawulu za tă yi aure da Dawuda, sai aka aurar da ita wa Adriyel na Mehola.
20 And Michal Saul's daughter loved David: and they told Saul, and the thing pleased him.
Mikal’yar Shawulu kuwa tana ƙaunar Dawuda sosai. Da aka gaya wa Shawulu labarin, sai ya yi farin ciki, ya yi tunani ya ce,
21 And Saul said, I will give her to him, that she may be a snare to him, and that the hand of the Philistines may be against him. Wherefore Saul said to David, Thou shalt this day be my son-in-law, in [the one of] the two.
“Zan ba shi ita tă zama masa tarko, da haka Filistiyawa za su same shi.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Yanzu kana da dama sau na biyu ka zama surukina.”
22 And Saul commanded his servants, [saying], Commune with David secretly, and say, Behold, the king hath delight in thee, and all his servants love thee: now therefore be the king's son-in-law.
Sai Shawulu ya umarci ma’aikatansa cewa, “Ku yi magana da Dawuda asirce ku ce, ‘Duba, sarki yana farin ciki da kai, dukan ma’aikatansa kuma suna sonka, ka yarda ka zama surukinsa.’”
23 And Saul's servants spoke those words in the ears of David. And David said, Seemeth it to you [a] light [thing] to be a king's son-in-law, seeing that I [am] a poor man, and lightly esteemed?
Suka sāke yi wa Dawuda wannan magana amma Dawuda ya ce, “Kuna tsammani abu mai sauƙi ne mutum yă zama surukin sarki? Ni talaka ne, kuma ba sananne ba.”
24 And the servants of Saul told him, saying, On this manner spoke David.
Da ma’aikatan Shawulu suka gaya masa abin da Dawuda ya faɗa.
25 And Saul said, Thus shall ye say to David, The king desireth not any dower, but a hundred foreskins of the Philistines, to be avenged of the king's enemies. But Saul thought to make David fall by the hand of the Philistines.
Sai Shawulu ya ce, “Ku gaya wa Dawuda, ‘Sarki ba ya bukatan kuɗin auren’yarsa, sai dai loɓar Filistiyawa domin ramako a kan abokan gābansa.’” Shawulu yana shiri ne domin Dawuda yă fāɗa a hannun Filistiyawa.
26 And when his servants told David these words, it pleased David well to be the king's son-in-law: and the days had not expired.
Da ma’aikatan suka gaya wa Dawuda waɗannan abubuwa, sai ya yi murna don zai zama surukin sarki. Amma kafin lokacin yă cika,
27 Wherefore David arose and went, he and his men, and slew of the Philistines two hundred men; and David brought their foreskins, and they gave them in full number to the king, that he might be the king's son-in-law. And Saul gave him Michal his daughter for a wife.
Dawuda da mutanensa suka fita suka kashe Filistiyawa ɗari biyu, suka kawo loɓar suka miƙa wa sarki, domin yă zama surukin sarki. Sai Shawulu ya ba da’yarsa Mikal aure ga Dawuda.
28 And Saul saw and knew that the LORD [was] with David, and [that] Michal, Saul's daughter, loved him.
Da Shawulu ya gane Ubangiji yana tare da Dawuda,’yarsa Mikal kuma tana ƙaunarsa,
29 And Saul was yet the more afraid of David; and Saul became David's enemy continually.
sai Shawulu ya ƙara jin tsoron Dawuda har ya zama maƙiyinsa a dukan sauran rayuwarsa.
30 Then the princes of the Philistines went forth: and it came to pass after they went forth, [that] David behaved himself more wisely than all the servants of Saul; so that his name was much esteemed.
Manyan sojojin Filistiyawa suka yi ta fita suna yaƙi da Isra’ilawa, amma kullum Dawuda yakan sami nasara fiye da sauran manyan sojojin Shawulu. Ta haka ya yi suna ƙwarai.