< 1 Peter 4 >

1 Forasmuch then as Christ hath suffered for us in the flesh, arm yourselves likewise with the same mind: for he that hath suffered in the flesh hath ceased from sin;
Saboda haka, tunda yake Almasihu ya sha wuya a jiki, muma mu sha damara da wannan ra'ayi. Duk wanda ya sha wuya a jiki ya daina aikata zunubi.
2 That he no longer should live the rest of [his] time in the flesh to the lusts of men, but to the will of God.
Wannan mutum kuma baya kara zaman biye wa muguwar sha'awar mutumtaka, amma sai dai nufin Allah dukkan sauran kwanakinsa a duniya.
3 For the time past of [our] life may suffice us to have wrought the will of the Gentiles, when we walked in lasciviousness, lusts, excess of wine, revelings, banquetings, and abominable idolatries:
Gama lokaci ya wuce da zamu yi abin da al'ummai suke son yi, wato fajirci, mugayen sha'awace-sha'awace, da buguwa da shashanci da shaye-shaye da bautar gumaku da abubuwan kyama.
4 In which they think it strange that ye run not with [them] to the same excess of riot, speaking evil of [you]:
Suna tunanin bakon abu ku ke yi da ba kwa hada kai tare da su yanzu a yin wadannan abubuwa, sai suna zarginku.
5 Who shall give account to him that is ready to judge the living and the dead.
Za su bada lissafi ga wanda yake a shirye ya shari'anta masu rai da matattu.
6 For, for this cause was the gospel preached also to them that are dead, that they might be judged according to men in the flesh, but live according to God in the spirit.
Shi yasa aka yi wa matattu wa'azin bishara, cewa ko da shike anyi masu shari'a cikin jikunan mutane, su rayu bisa ga Allah a ruhu.
7 But the end of all things is at hand: be ye therefore sober, and watch to prayer.
Karshen dukkan abubuwa yana gabatowa. Saboda haka, ku zama natsatsu, ku natsu cikin tunaninku domin yin addu'oi.
8 And above all things have fervent charity among yourselves: for charity will cover a multitude of sins.
Gaba da kome, ku himmatu wajen kaunar juna, domin kauna bata neman tona zunuban wadansu.
9 Use hospitality one to another without grudging.
Ku yi wa juna bakunta da abubuwa nagari ba tare da gunaguni ba.
10 As every man hath received the gift, [even so] minister the same one to another, as good stewards of the manifold grace of God.
Yadda kowanne dayanku ya sami baiwa, kuyi amfani da su domin ku kyautata wa juna, kamar masu rikon amanar bayebaye na Allah, wanda ya ba mu hannu sake.
11 If any man speaketh [let him speak] as the oracles of God; if any man ministereth [let him do it] as of the ability which God giveth: that God in all things may be glorified through Jesus Christ; to whom be praise and dominion for ever and ever. Amen. (aiōn g165)
Idan wani yana yin wa'azi, ya zamana fadar Allah ya ke fadi, idan wani yana hidima, ya yi da karfin da Allah ya ba shi, domin cikin dukkan abubuwa a daukaka Allah ta wurin Yesu Almasihu. Daukaka da iko nasa ne har abada abadin. Amin. (aiōn g165)
12 Beloved, think it not strange concerning the fiery trial which is to try you, as though some strange thing happened to you:
Ya kaunatattu, kada ku zaci cewa matsananciyar wahalar da ta zo ta gwada ku bakon abu ne, ko kuma wani bakon abu ne yake faruwa a gareku.
13 But rejoice, seeing ye are partakers of Christ's sufferings; that, when his glory shall be revealed, ye may be glad also with exceeding joy.
Amma muddin kuna tarayya da Almasihu cikin wahalarsa, ku yi murna, domin kuyi farin ciki da murna sa'adda za a bayyana daukakarsa.
14 If ye are reproached for the name of Christ, happy [are ye]; for the spirit of glory and of God resteth upon you. On their part he is evil spoken of, but on your part he is glorified.
Idan ana zargin ku sabili da sunan Almasihu, ku masu albarka ne, domin Ruhun daukaka da Ruhun Allah ya tabbata a kanku.
15 But let none of you suffer as a murderer, or [as] a thief, or [as] an evil-doer, or as a busy-body in other men's matters.
Amma kada kowannen ku ya sha wahala sabo da horon shi mai kisan kai ne, ko barawo, ko mamugunci, ko mai shisshigi.
16 Yet if [any man suffereth] as a Christian, let him not be ashamed; but let him glorify God on this behalf.
Amma in wani yana shan wahala sabili da shi na Almasihu ne, kada ya ji kunya, amma ya daukaka Allah a wannan sunan.
17 For the time [is come] that judgment must begin at the house of God: and if [it] first [beginneth] at us, what will [be] the end of them that obey not the gospel of God?
Domin lokaci ya yi da shari'a za ta fara daga gidan iyalin Allah. Idan kuwa za a fara da mu, menene karshen wadanda suka ki biyayya da bisharar Allah?
18 And if the righteous is scarcely saved, where will the ungodly and the sinner appear?
Idan mutum, “mai adalci ya tsira da kyar, to, me zai faru da marar bin Allah da mai zunubi kuma?”
19 Wherefore, let them that suffer according to the will of God, commit the keeping of their souls [to him] in well-doing, as to a faithful Creator.
Sabo da haka bari wadanda suke shan wuya bisa ga nufin Allah, su mika rayukansu ga amintaccen Mahalicci suna kuma yin ayyuka nagari.

< 1 Peter 4 >