< 1 Corinthians 11 >
1 Be ye followers of me, even as I also [am] of Christ.
Ku bi gurbina, kamar yadda ni nake bin gurbin Kiristi.
2 Now I praise you, brethren, that ye remember me in all things, and keep the ordinances, as I delivered [them] to you.
Ina yabonku saboda kuna tunawa da ni a cikin kowane abu, kuna kuma riƙe da koyarwar, yadda na ba ku.
3 But I would have you know, that the head of every man is Christ; and the head of the woman [is] the man; and the head of Christ [is] God.
To, ina so ku gane cewa shugaban kowane namiji Kiristi ne, shugaban mace namiji ne, shugaban Kiristi kuma Allah ne.
4 Every man praying or prophesying, having [his] head covered, dishonoreth his head.
Kowane namijin da ya yi addu’a ko annabci da kansa a rufe ya jawo kunya wa kansa.
5 But every woman that prayeth or prophesieth with [her] head uncovered, dishonoreth her head: for that is even all one as if she were shaved.
Duk macen da ta yi addu’a ko annabci da kanta a buɗe kuwa ta rena kanta, ya zama kamar an aske kanta ke nan.
6 For if the woman is not covered, let her also be shorn: but if it is a shame for a woman to be shorn or shaved, let her be covered.
In mace ba ta so tă rufe kanta, to, sai tă aske gashinta; in kuwa abin kunya ne mace tă yanke ko tă aske gashinta, to, sai tă rufe kanta.
7 For a man indeed ought not to cover [his] head, forasmuch as he is the image and glory of God: but the woman is the glory of the man.
Namiji kuwa bai kamata ya rufe kansa ba, da yake shi kamannin Allah ne, da kuma darajar Allah, amma mace dai, darajar namiji ne.
8 For the man is not from the woman, but the woman from the man.
Gama namiji bai fito daga mace ba, sai dai mace ce ta fito daga namiji.
9 Neither was the man created for the woman, but the woman for the man.
Ba a kuma halicci namiji don mace ba, sai dai mace don namiji.
10 For this cause ought the woman to have power on [her] head, because of the angels.
Don haka, saboda wannan, da kuma saboda mala’iku, dole mace ta ɗaura wani abu a kanta.
11 Nevertheless, neither is the man without the woman, neither the woman without the man in the Lord.
Duk da haka a cikin Ubangiji, mace ba a rabe take da namiji ba, namiji kuma ba a rabe yake da mace ba.
12 For as the woman [is] from the man, even so [is] the man also by the woman; but all things from God.
Kamar yadda mace ta fito daga namiji, haka kuma aka haifi namiji ta wurin mace. Sai dai kowane abu daga Allah yake.
13 Judge in yourselves: Is it comely that a woman should pray to God uncovered?
Ku kanku duba mana. Ya yi kyau mace tă yi addu’a ga Allah da kanta a buɗe?
14 Doth not even nature itself teach you, that if a man hath long hair, it is a shame to him?
Kai, yadda halitta take ma, ai, ta koya muku cewa in namiji yana da dogon gashi, abin kunya ne a gare shi,
15 But if a woman hath long hair, it is a glory to her: for [her] hair is given her for a covering.
amma in mace tana da dogon gashi, ai, daraja ce a gare ta. Gama an ba ta dogon gashi saboda rufe kanta ne.
16 But if any man seemeth to be contentious, we have no such custom, neither the churches of God.
In akwai mai gardama da wannan, to, mu dai ba mu da wata al’ada, haka ma ikkilisiyoyin Allah.
17 Now in this that I declare [to you], I praise [you] not, that ye come together not for the better, but for the worse.
Game da umarnan nan dai, ban yaba muku ba, domin taruwarku ba ta kirki ba ce, ɓarna ce.
18 For first of all, when ye come together in the church, I hear that there are divisions among you; and I partly believe it.
Da farko dai, na ji cewa sa’ad da kuka taru a matsayin ikkilisiya, akwai tsattsaguwa a tsakaninku, har na fara yarda da zancen.
19 For there must be also heresies among you, that they who are approved may be made manifest among you.
Ba shakka dole a sami bambanci a tsakaninku don a nuna wa Allah ya amince da shi a cikinku.
20 When therefore ye come together in one place, [this] is not to eat the Lord's supper.
Sa’ad da kuka taru, ba Cimar Ubangiji kuke ci ba,
21 For in eating every one taketh before [another] his own supper: and one is hungry, and another is drunken.
gama yayinda kuke ci, kowa yakan ci gaba ba tare da jiran wani ba. Wani yă zauna da yunwa, wani kuma yă bugu.
22 What? have ye not houses to eat and to drink in? or despise ye the church of God, and shame them that have not? What shall I say to you? shall I praise you in this? I praise [you] not.
Kai, ba ku da gidajen da za ku ci ku sha ne? Ko dai kun rena ikkilisiyar Allah ne, kuna kuma wulaƙanta waɗanda ba su da kome? Me zan ce muku? In yabe ku ne game da wannan? A’a, ko kaɗan!
23 For I have received from the Lord, that which also I delivered to you, That the Lord Jesus, the [same] night in which he was betrayed, took bread:
Gama abin da na karɓa daga wurin Ubangiji shi ne nake ba ku. Ubangiji Yesu, a daren da aka bashe shi, ya ɗauki burodi,
24 And when he had given thanks, he broke [it], and said, Take, eat: this is my body, which is broken for you: this do in remembrance of me.
bayan ya yi godiya, sai ya kakkarya ya ce, “Wannan jikina ne, wanda yake dominku, ku yi wannan don tunawa da ni.”
25 After the same manner also [he took] the cup, when he had supped, saying, This cup is the new testament in my blood: this do ye, as often as ye drink [it], in remembrance of me.
Haka kuma bayan cimar, ya ɗauki kwaf, yana cewa, “Wannan kwaf ne sabon alkawari a jinina; ku yi wannan, a duk sa’ad da kuke sha, don tunawa da ni.”
26 For as often as ye eat this bread, and drink this cup, ye do show the Lord's death till he shall come.
Gama a duk sa’ad da kuke cin wannan burodi, kuke kuma sha daga wannan kwaf, kuna shelar mutuwar Ubangiji ne har yă dawo.
27 Wherefore, whoever shall eat this bread, and drink [this] cup of the Lord unworthily, shall be guilty of the body and blood of the Lord.
Saboda haka, duk wanda ya ci burodin ko ya sha daga kwaf na Ubangiji da rashin cancanta, ya yi laifin wulaƙanta jiki da jinin Ubangiji ke nan.
28 But let a man examine himself, and so let him eat of [that] bread, and drink of [that] cup.
Dole kowa yă bincike kansa kafin yă ci burodin yă kuma sha daga kwaf ɗin.
29 For he that eateth and drinketh unworthily, eateth and drinketh condemnation to himself, not discerning the Lord's body.
Gama duk wanda ya ci ya kuma sha ba tare da fahimtar jikin Ubangiji ba, ya ci ya kuma sha wa kansa hukunci ne.
30 For this cause many [are] weak and sickly among you, and many sleep.
Shi ya sa da yawa a cikinku ba su da ƙarfi, suna kuma da rashin lafiya, waɗansunku kuma sun riga sun yi barci.
31 For if we would judge ourselves, we should not be judged.
Amma in da za mu auna kanmu sosai, da ba za mu shiga irin hukuncin nan ba.
32 But when we are judged, we are chastened by the Lord, that we should not be condemned with the world.
Duk da haka sa’ad da Ubangiji ya hukunta mu, ana yin mana horo ne don kada a ƙarshe a hallaka mu tare da duniya.
33 Wherefore, my brethren, when ye come together to eat, tarry one for another.
Saboda haka’yan’uwana, sa’ad da kuka taru don ci, ku jira juna.
34 And if any man hungereth, let him eat at home; that ye come not together to condemnation. And the rest will I set in order when I come.
In wani yana jin yunwa, sai yă ci abinci a gida, saboda in kuka taru kada yă jawo hukunci. Sa’ad da na zo kuma zan ba da ƙarin umarnai.