< 1 Corinthians 1 >

1 Paul, called [to be] an apostle of Jesus Christ through the will of God, and Sosthenes [our] brother,
Bulus, kirayayye daga Almsihu Yesu don zama manzo ta wurin nufin Allah, da dan'uwanmu Sastanisu,
2 To the church of God which is at Corinth, to them that are sanctified in Christ Jesus, called [to be] saints, with all that in every place call upon the name of Jesus Christ our Lord, both theirs and ours.
zuwa ga Ikilisiyar Allah da ke korinti, zuwa ga wadanda aka kebe su cikin Almasihu Yesu, wadanda aka kira domin su zama al'umma maitsarki. Muna kuma rubuta wa dukan masu kira bisa sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu a ko'ina, wato Ubangijinsu da Ubangijinmu kuma.
3 Grace [be] to you, and peace from God our Father, and [from] the Lord Jesus Christ.
Bari alheri da salama su zo gare ku daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Almasihu.
4 I thank my God always on your behalf, for the grace of God which is given you by Jesus Christ;
Kodayaushe ina gode wa Allahna domin ku, saboda alherin Allah da Almasihu Yesu ya yi maku.
5 That in every thing ye are enriched by him, in all utterance, and [in] all knowledge;
Ya ba ku arziki ta kowace hanya, cikin dukkan magana da dukkan ilimi.
6 Even as the testimony of Christ was confirmed in you:
Kamar yadda shaida game da Almasihu ta tabbata gaskiya a tsakaninku.
7 So that ye come behind in no gift; waiting for the coming of our Lord Jesus Christ:
Saboda haka baku rasa wata baiwa ta ruhaniya ba yayinda kuke marmarin jiran bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Almasihu.
8 Who will also confirm you to the end, [that ye may be] blameless in the day of our Lord Jesus Christ.
Zai kuma karfafa ku zuwa karshe, saboda ku zama marasa aibi a ranar Ubangijinmu Yesu Almasihu.
9 God [is] faithful, by whom ye were called to the fellowship of his Son Jesus Christ our Lord.
Allah mai aminci ne shi wanda ya kira ku zuwa zumunta ta Dansa, Yesu Almasihu Ubangijimu.
10 Now I beseech you, brethren, by the name of our Lord Jesus Christ, that ye all speak the same thing, and [that] there be no divisions among you; but [that] ye be perfectly joined together in the same mind, and in the same judgment.
Ina rokon ku, yan'uwa, cikin sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu, ku yarda da juna, kada tsattsaguwa ta kasance tsakanin ku. Ina rokon ku ku zama da zuciya daya da kuma nufi daya.
11 For it hath been declared to me concerning you, my brethren, by them [who are of the house] of Chloe, that there are contentions among you.
Gama mutanen gidan Kulowi sun kawo kara cewa akwai tsattsaguwa a cikin ku.
12 Now this I say, that every one of you saith, I am of Paul; and I of Apollos; and I of Cephas; and I of Christ.
Ina nufin: kowannen ku na cewa, “Ina bayan Bulus,” ko “Ina bayan Afollos,” ko “Ina bayan Kefas,” ko “Ina bayan Almasihu.”
13 Is Christ divided? was Paul crucified for you? or were ye baptized in the name of Paul?
Almasihu a rarrabe yake? An gicciye Bulus domin ku? Ko an yi maku baftisma a cikin sunan Bulus?
14 I thank God that I baptized none of you, but Crispus and Gaius;
Na godewa Allah domin ban yi wa wanin ku baftisma ba, sai dai Kirisfus da Gayus.
15 Lest any should say that I had baptized in my own name.
Na yi wannan saboda kada wani ya ce an yi maku baftisma a cikin sunana.
16 And I baptized also the household of Stephanas; besides, I know not whether I baptized any other.
(Na kuma yi wa iyalin gidan Sitifanas baftisma. Banda haka, ban sani ko na yi wa wani baftisma ba.)
17 For Christ hath not sent me to baptize, but to preach the gospel: not with wisdom of words, lest the cross of Christ should be made of no effect.
Gama Almasihu bai aiko ni domin yin baftisma ba, amma domin yin wa'azin bishara. Bai aiko ni domin in yi wa'azi da kalmomin hikimar mutum ba, saboda kada giciyen Almasihu ya rasa ikonsa.
18 For the preaching of the cross is to them that perish, foolishness; but to us who are saved, it is the power of God.
Gama wa'azin gicciye wauta ne ga wadanda su ke mutuwa. Amma cikin wadanda Allah ke ceto, ikon Allah ne.
19 For it is written, I will destroy the wisdom of the wise, and will bring to nothing the understanding of the prudent.
Gama a rubuce yake, “Zan watsar da hikimar masu hikima. Zan dode fahimtar masu basira.”
20 Where [is] the wise? where [is] the scribe? where [is] the disputer of this world? hath not God made foolish the wisdom of this world? (aiōn g165)
Ina mai hikima? Ina masani? Ina mai muhawara na duniyan nan? Allah bai juya hikimar duniya zuwa wauta ba? (aiōn g165)
21 For when in the wisdom of God the world by wisdom knew not God, it pleased God by the foolishness of preaching to save them that believe.
Tunda duniya cikin hikimarta bata san Allah ba, ya gamshi Allah ta wurin wautar wa'azi ya ceci masu bada gaskiya.
22 For the Jews require a sign, and the Greeks seek wisdom:
Gama Yahudawa suna bidar al'ajibai, Helinawa kuma suna neman hikima.
23 But we preach Christ crucified, to the Jews a stumbling-block, and to the Greeks foolishness;
Amma muna wa'azin Almasihu gicciyayye, dutsen tuntube ga yahudawa da kuma wauta ga Helinawa.
24 But to them who are called, both Jews and Greeks, Christ the power of God, and the wisdom of God.
Amma ga wadanda Allah ya kira, Yahudawa da Helinawa, muna wa'azin Almasihu a matsayin iko da kuma hikimar Allah.
25 Because the foolishness of God is wiser than men; and the weakness of God is stronger than men.
Gama wautar Allah tafi mutane hikima, kuma rashin karfin Allah yafi mutane karfi.
26 For ye see your calling, brethren, that not many wise men after the flesh, not many mighty, not many noble [are called]:
Dubi kiranku, yan'uwa. Ba dukkan ku ke da hikima a ma'aunin mutane ba. Ba dukkan ku ke da iko ba. Ba dukkan ku ke da haifuwa ta sarauta ba.
27 But God hath chosen the foolish things of the world to confound the wise; and God hath chosen the weak things of the world to confound the things which are mighty;
Amma Allah ya zabi abubuwan da suke wofi na duniya domin ya kunyatar da masu hikima. Allah ya zabi abin da ke marar karfi a duniya domin ya kunyatar da abinda ke mai karfi.
28 And base things of the world, and things which are despised, hath God chosen, and things which are not, to bring to naught things that are:
Allah ya zabi abinda ke marar daraja da kuma renanne a duniya. Ya ma zabi abubuwan da ake dauka ba komai ba, domin ya wofinta abubuwan da ake dauka masu daraja.
29 That no flesh should glory in his presence.
Ya yi wannan ne domin kada wani ya sami dalilin fahariya a gabansa.
30 But of him are ye in Christ Jesus, who from God is made to us wisdom, and righteousness, and sanctification, and redemption:
Domin abinda Allah ya yi, yanzu kuna cikin Almasihu Yesu, wanda ya zamar mana hikima daga Allah. Ya zama adalcinmu, da tsarkinmu da fansarmu.
31 That, according as it is written, He that glorieth, let him glory in the Lord.
A sakamakon haka, kamar yadda nassi ya ce, “Bari mai yin fahariya, ya yi fahariya cikin Ubangiji.”

< 1 Corinthians 1 >