< 1 Chronicles 16 >
1 So they brought the ark of God, and set it in the midst of the tent that David had pitched for it: and they offered burnt-sacrifices and peace-offerings before God.
Suka fa kawo akwatin alkawarin Allah, suka sa a cikin tentin da Dawuda ya kafa dominsa, suka kuma miƙa hadayun ƙonawa da hadayu na salama a gaban Allah.
2 And when David had made an end of offering the burnt-offerings and the peace-offerings, he blessed the people in the name of the LORD.
Bayan Dawuda ya gama miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji.
3 And he dealt to every one of Israel, both man and woman, to every one a loaf of bread, and a good piece of flesh, and a flagon [of wine].
Sa’an nan ya ba da dunƙulen burodi da wainar dabino da kuma kauɗar zabibi ga kowane mutumin Isra’ila namiji da ta mace.
4 And he appointed [certain] of the Levites to minister before the ark of the LORD, and to record, and to thank and praise the LORD God of Israel:
Ya sa Lawiyawa su yi hidima a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, su ɗaukaka, su gode, su kuma yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
5 Asaph the chief, and next to him Zechariah, Jeiel, and Shemiramoth, and Jehiel, and Mattithiah, and Eliab, and Benaiah, and Obed-edom: and Jeiel with psalteries and with harps; but Asaph made a sound with cymbals;
Asaf shi ne babba, sai Zakariya na biye, sa’an nan Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Mattitiya, Eliyab, Benahiya, Obed-Edom da Yehiyel. Su ne za su kaɗa molaye, da garayu, Asaf kuwa zai buga ganguna,
6 Benaiah also and Jahaziel the priests with trumpets continually before the ark of the covenant of God.
Benahiya da Yahaziyel firistoci za su busa ƙahoni kullum a gaban akwatin alkawarin Allah.
7 Then on that day David delivered first [this psalm] to thank the LORD into the hand of Asaph and his brethren.
A wannan rana, da farko, Dawuda ya sa Asaf da’yan’uwansa su rera wannan zabura ta yabo ga Ubangiji.
8 Give thanks to the LORD, call upon his name, make known his deeds among the people.
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
9 Sing to him, sing psalms to him, talk ye of all his wonderous works.
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan ayyukan banmamakinsa.
10 Glory ye in his holy name: let the heart of them rejoice that seek the LORD.
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
11 Seek the LORD and his strength, seek his face continually.
Ku dogara ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
12 Remember his wonderful works that he hath done, his wonders, and the judgments of his mouth;
Ku tuna ayyukan banmamakin da ya aikata, mu’ujizansa da kuma hukuntai da ya yanke,
13 O ye seed of Israel his servant, ye children of Jacob, his chosen ones.
Ya ku zuriyar Isra’ila bayinsa, Ya ku’ya’yan Yaƙub maza, zaɓaɓɓunsa.
14 He [is] the LORD our God; his judgments [are] in all the earth.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; hukuntansa suna a cikin dukan duniya.
15 Be ye mindful always of his covenant; the word [which] he commanded to a thousand generations;
Yakan tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
16 [Even of the covenant] which he made with Abraham, and of his oath to Isaac;
alkawarin da ya yi wa Ibrahim rantsuwar da ya yi ga Ishaku.
17 And which he confirmed to Jacob for a law, [and] to Israel [for] an everlasting covenant,
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub kamar ƙa’ida, ga Isra’ila kamar madawwamin alkawari.
18 Saying, To thee will I give the land of Canaan, the lot of your inheritance;
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana kamar rabon da za ka gāda.”
19 When ye were but few, even a few, and strangers in it.
Sa’ad da suke kima, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
20 And [when] they went from nation to nation, and from [one] kingdom to another people;
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga wannan mulki zuwa wancan.
21 He suffered no man to do them wrong: yea, he reproved kings for their sakes,
Bai bar wani ya zalunce su ba; saboda su ya tsawata wa sarakuna.
22 [Saying], Touch not my anointed, and do my prophets no harm.
“Kada ku taɓa shafaffuna; kada ku yi wa annabawana lahani.”
23 Sing to the LORD, all the earth; show forth from day to day his salvation.
Ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
24 Declare his glory among the heathen; his wonderful works among all nations.
Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, ayyukansa masu al’ajabai a cikin mutane.
25 For great [is] the LORD, and greatly to be praised: he also [is] to be feared above all gods.
Gama Ubangiji mai girma ne ya kuma cancanci yabo; dole a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
26 For all the gods of the people [are] idols: but the LORD made the heavens.
Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ya yi sammai.
27 Glory and honor [are] in his presence; strength and gladness [are] in his place.
Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da farin ciki suna a wurin zamansa.
28 Give to the LORD, ye kindreds of the people, give to the LORD glory and strength.
Ku yabi Ubangiji, ku iyalan al’ummai, ku yabi ɗaukaka da ƙarfin Ubangiji,
29 Give to the LORD the glory [due] to his name: bring an offering, and come before him: worship the LORD in the beauty of holiness.
ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa. Ku kawo hadaya ku kuma zo gabansa; ku yi wa Ubangiji sujada cikin darajar tsarkinsa.
30 Fear before him, all the earth: the world also shall be stable, that it be not moved.
Ku yi rawar jiki a gabansa, ya ku duniya duka! Duniya ta kahu sosai; ba za tă jijjigu ba.
31 Let the heavens be glad, and let the earth rejoice: and let [men] say among the nations, The LORD reigneth.
Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari su ce a cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki!”
32 Let the sea roar, and the fullness thereof: let the fields rejoice, and all that [is] therein.
Bari teku da kome da yake cikinsa su yi ruri; bari gonaki da kome a cikinsu su yi farin ciki!
33 Then shall the trees of the wood sing at the presence of the LORD, because he cometh to judge the earth.
Sa’an nan itatuwan jeji za su rera, za su rera don farin ciki a gaban Ubangiji, gama ya zo don yă hukunta duniya.
34 O give thanks to the LORD; for [he is] good; for his mercy [endureth] for ever.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama shi nagari ne; ƙaunarsa madawwamiya ce.
35 And say ye, Save us, O God of our salvation, and gather us together, and deliver us from the heathen, that we may give thanks to thy holy name, [and] glory in thy praise.
Ku yi kuka, ku ce, “Cece mu, ya Allah Mai Cetonmu; tara mu ka kuma cece mu daga al’ummai, don mu yi godiya ga sunanka mai tsarki, don mu ɗaukaka a cikin yabonka.”
36 Blessed [be] the LORD God of Israel for ever and ever. And all the people said, Amen, and praised the LORD.
Yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Sai dukan mutane suka ce, “Amin.” Suka kuma “Yabi Ubangiji.”
37 So he left there before the ark of the covenant of the LORD Asaph and his brethren, to minister before the ark continually, as every day's work required:
Dawuda ya bar Asaf da’yan’uwansa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji don su yi hidima a can kullum, bisa ga tsari na kowace rana.
38 And Obed-edom with their brethren, sixty and eight; Obed-edom also the son of Jeduthun and Hosah [to be] porters:
Ya kuma bar Obed-Edom da’yan’uwansa sittin da takwas don su yi hidima tare. Obed-Edom ɗan Yedutun da Hosa kuma, su ne matsaran ƙofofi.
39 And Zadok the priest, and his brethren the priests, before the tabernacle of the LORD in the high place that [was] at Gibeon,
Dawuda ya bar Zadok firist da’yan’uwansa firistoci a gaban tabanakul na Ubangiji a tudun da yake a Gibeyon
40 To offer burnt-offerings to the LORD upon the altar of the burnt-offering continually morning and evening, and [to do] according to all that is written in the law of the LORD, which he commanded Israel;
don su miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a kan bagaden hadaya ta ƙonawa kullum, da safe da kuma yamma, bisa ga kome da yake a rubutacce a cikin Dokar Ubangiji, da ya ba wa Isra’ila.
41 And with them Heman and Jeduthun, and the rest that were chosen, who were expressed by name, to give thanks to the LORD, because his mercy [endureth] for ever;
Tare da su akwai Heman da Yedutun da sauran waɗannan zaɓaɓɓun da aka rubuta sunansu don yin godiya ga Ubangiji, “gama ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
42 And with them Heman and Jeduthun with trumpets and cymbals for those that should make a sound, and with musical instruments of God. And the sons of Jeduthun [were] porters.
Heman da Yedutun su ne da hakkin busa ƙahoni da kaɗa kuge da sauran kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda ake amfani da su lokacin da ake rera waƙoƙi masu tsarki.’Ya’yan Yedutun maza, su aka ba wa aikin tsaron ƙofa.
43 And all the people departed every man to his house: and David returned to bless his house.
Sa’an nan dukan mutanen suka tashi, kowa ya koma gidansa, Dawuda ya koma gida yă sa wa iyalinsa albarka.