< Psalms 7 >

1 Shiggaion of David, which he sang to the LORD, concerning the words of Cush the Benjamite. O LORD my God, in thee do I put my trust: save me from all them that persecute me, and deliver me:
Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
2 Lest he tear my soul like a lion, rending it in pieces, while there is none to deliver.
in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
3 O LORD my God, if I have done this; if there is iniquity in my hands;
Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
4 If I have rewarded evil to him that was at peace with me; (yea, I have delivered him that without cause is my enemy: )
in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
5 Let the enemy persecute my soul, and take it; yea, let him tread down my life upon the earth, and lay my honour in the dust. (Selah)
to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
6 Arise, O LORD, in thy anger, lift up thyself because of the rage of my enemies: and awake for me to the judgment that thou hast commanded.
Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
7 So shall the congregation of the people surround thee: for their sakes therefore return thou on high.
Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
8 The LORD shall judge the people: judge me, O LORD, according to my righteousness, and according to my integrity that is in me.
bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
9 O let the wickedness of the wicked come to an end; but establish the just: for the righteous God trieth the hearts and reins.
Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
10 My defence is from God, who saveth the upright in heart.
Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
11 God judgeth the righteous, and God is angry with the wicked every day.
Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
12 If he turn not, he will whet his sword; he hath bent his bow, and made it ready.
In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
13 He hath also prepared for him the instruments of death; he ordaineth his arrows against the persecutors.
Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
14 Behold, he travaileth with iniquity, and hath conceived mischief, and brought forth falsehood.
Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
15 He made a pit, and dug it, and hath fallen into the ditch which he made.
Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
16 His mischief shall return upon his own head, and his violent dealing shall come down upon the crown of his head.
Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
17 I will praise the LORD according to his righteousness: and will sing praise to the name of the LORD most high.
Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.

< Psalms 7 >