< Psalms 55 >

1 To the chief Musician on Neginoth, Maschil, A Psalm of David. Give ear to my prayer, O God; and hide not thyself from my supplication.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
2 Attend to me, and hear me: I mourn in my complaint, and make a noise;
ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
3 Because of the voice of the enemy, because of the oppression of the wicked: for they cast iniquity upon me, and in wrath they hate me.
hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
4 My heart is greatly pained within me: and the terrors of death have fallen upon me.
Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
5 Fearfulness and trembling have come upon me, and horror hath overwhelmed me.
Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
6 And I said, O that I had wings like a dove! for then I would fly away, and be at rest.
Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
7 Lo, then I would wander far off, and remain in the wilderness. (Selah)
da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
8 I would hasten my escape from the windy storm and tempest.
da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
9 Destroy, O Lord, and divide their tongues: for I have seen violence and strife in the city.
Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
10 Day and night they go about her upon her walls: mischief also and sorrow are in her midst.
Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
11 Wickedness is in her midst: deceit and guile depart not from her streets.
Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
12 For it was not an enemy that reproached me; then I could have borne it: neither was it he that hated me that magnified himself against me; then I would have hid myself from him:
Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
13 But it was thou, a man my equal, my guide, and my acquaintance.
Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
14 We took sweet counsel together, and walked to the house of God in company.
wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
15 Let death seize upon them, and let them go down alive into hell: for wickedness is in their dwellings, and among them. (Sheol h7585)
Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol h7585)
16 As for me, I will call upon God; and the LORD shall save me.
Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
17 Evening, and morning, and at noon, will I pray, and cry aloud: and he shall hear my voice.
Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
18 He hath delivered my soul in peace from the battle that was against me: for there were many with me.
Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
19 God shall hear, and afflict them, even he that abideth of old. (Selah) Because they have no changes, therefore they fear not God.
Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
20 He hath put forth his hands against such as are at peace with him: he hath broken his covenant.
Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
21 The words of his mouth were smoother than butter, but war was in his heart: his words were softer than oil, yet were they drawn swords.
Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
22 Cast thy burden upon the LORD, and he shall sustain thee: he shall never allow the righteous to be moved.
Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
23 But thou, O God, shalt bring them down into the pit of destruction: bloody and deceitful men shall not live out half their days; but I will trust in thee.
Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.

< Psalms 55 >