< Psalms 33 >

1 Rejoice in the LORD, O ye righteous: for praise is comely for the upright.
Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
2 Praise the LORD with harp: sing to him with the psaltery and an instrument of ten strings.
Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
3 Sing to him a new song; play skilfully with a loud noise.
Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
4 For the word of the LORD is right; and all his works are done in truth.
Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
5 He loveth righteousness and judgment: the earth is full of the goodness of the LORD.
Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
6 By the word of the LORD were the heavens made; and all the host of them by the breath of his mouth.
Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
7 He gathereth the waters of the sea together as an heap: he layeth up the depth in store houses.
Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
8 Let all the earth fear the LORD: let all the inhabitants of the world stand in awe of him.
Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
9 For he spoke, and it was done; he commanded, and it stood fast.
Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
10 The LORD bringeth the counsel of the heathen to nought: he maketh the devices of the people of no effect.
Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
11 The counsel of the LORD standeth for ever, the thoughts of his heart to all generations.
Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
12 Blessed is the nation whose God is the LORD; and the people whom he hath chosen for his own inheritance.
Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
13 The LORD looketh from heaven; he beholdeth all the sons of men.
Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
14 From the place of his habitation he looketh upon all the inhabitants of the earth.
daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
15 He fashioneth their hearts alike; he considereth all their works.
shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
16 There is no king saved by the multitude of an host: a mighty man is not delivered by much strength.
Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
17 An horse is a vain thing for safety: neither shall he deliver any by his great strength.
Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
18 Behold, the eye of the LORD is upon them that fear him, upon them that hope in his mercy;
Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
19 To deliver their soul from death, and to keep them alive in famine.
don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
20 Our soul waiteth for the LORD: he is our help and our shield.
Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
21 For our heart shall rejoice in him, because we have trusted in his holy name.
A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
22 Let thy mercy, O LORD, be upon us, according as we hope in thee.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.

< Psalms 33 >