< Luke 3 >

1 Now in the fifteenth year of the reign of Tiberius Caesar, Pontius Pilate being governor of Judaea, and Herod being tetrarch of Galilee, and his brother Philip tetrarch of Ituraea and of the region of Trachonitis, and Lysanias the tetrarch of Abilene,
A cikin shekara ta goma sha biyar da Tibariyus Kaisar ke mulki, Bilatus Babunti kuma ke jagorar Yahudiya, Hirudus yana sarautar Galili, dan'uwansa Filibus yana sarautar yankin Ituriya da Tirakonitis, Lisaniyas kuma na sarautar yankin Abiliya,
2 Annas and Caiaphas being the high priests, the word of God came to John the son of Zacharias in the wilderness.
kuma zamanin da Hanana da Kayafa suke manyan firistoci, maganar Allah ta zo wurin Yahaya dan Zakariya, a cikin jeji.
3 And he came into all the country about Jordan, preaching the baptism of repentance for the remission of sins;
Ya yi tafiya cikin dukan yankuna da ke kewaye da Kogin Urdun, yana wa'azin baftismar tuba domin gafarar zunubai.
4 As it is written in the book of the words of Isaiah the prophet, saying, The voice of one crying in the wilderness, Prepare ye the way of the Lord, make his paths straight.
Kamar yadda aka rubuta a cikin littafin annabi Ishaya, “Ga muryan wani yana kira a cikin jeji, 'Shirya hanyar Ubangiji, ka daidaita tafarkunsa!
5 Every valley shall be filled, and every mountain and hill shall be brought low; and the crooked shall be made straight, and the rough ways shall be made smooth;
Za a cika kowani kwari, za a fasa kowani dutse a kuma baje kowani tudu, za a mike karkatattun hanyoyi, za a cike hanyoyi masu gargada,
6 And all flesh shall see the salvation of God.
kuma dukan mutane za su ga ceton Allah.”
7 Then said he to the multitude that came forth to be baptized by him, O generation of vipers, who hath warned you to flee from the wrath to come?
Sai Yahaya ya kara fada wa taron jama'ar da ke zuwa domin ya yi masu baftisma, “Ku 'ya'yan macizai masu dafi, wa ya gargadeku ku guje wa fushin nan mai zuwa?
8 Bring forth therefore fruits worthy of repentance, and begin not to say within yourselves, We have Abraham for our father: for I say to you, That God is able of these stones to raise up children to Abraham.
Ku ba da 'ya'ya da sun cancanci tuba, kada ku kuma fara cewa a cikinku, 'Muna da Ibrahim a matsayin Ubanmu', domin ina gaya maku, Allah yana iya ta da wa Ibrahim 'ya'ya daga cikin wadannan duwatsu.
9 And now also the axe is laid to the root of the trees: every tree therefore which bringeth not forth good fruit is hewn down, and cast into the fire.
Yanzu kuwa, an rigaya an sa gatari a gindin itatuwa. Sabili da haka, duk itacen da bai ba da 'ya'ya masu kyau ba za a sare shi kasa a kuma jefa shi cikin wuta.”
10 And the people asked him, saying, What shall we do then?
Sai mutanen da ke cikin taron jama'ar suka tambaye shi cewa, “To me za mu yi?”
11 He answereth and saith to them, He that hath two coats, let him impart to him that hath none; and he that hath food, let him do likewise.
Ya amsa ya ce masu, “Idan wani yana da taguwa biyu, sai ya ba wanda bashi da ita daya, kuma wanda yake da abinci ya yi haka nan.”
12 Then came also tax collectors to be baptized, and said to him, Master, what shall we do?
Masu karban haraji ma suka zo domin a yi masu baftisma, suka ce masa, “Malam, me za mu yi?”
13 And he said to them, Exact no more than that which is appointed you.
Ya ce masu, “Kada ku karba kudi fiye da yadda aka umarce ku.”
14 And the soldiers likewise asked him, saying, And what shall we do? And he said to them, Do violence to no man, neither accuse any falsely; and be content with your wages.
Wasu sojoji ma suka tambaye shi cewa, “To, mu fa? Yaya za mu yi?” Ya ce masu, “Kada ku kwace wa wani kudi, kada ku kuma yi wa wani zargin karya. Ku dogara ga albashinku.”
15 And as the people were in expectation, and all men mused in their hearts concerning John, whether he was the Christ, or not;
Ana nan da mutane ke sauraron zuwan Almasihu, kowa yana ta tunani a zuciyar sa game da Yahaya, ko shi ne Almasihu.
16 John answered, saying to them all, I indeed baptize you in water; but one mightier than I cometh, the latchet of whose shoes I am not worthy to loose: he shall baptize you in the Holy Spirit and in fire:
Yahaya ya amsa ya ce masu duka, “Game da ni dai, na yi maku baftisma da ruwa, amma akwai wani tafiye wanda ya fi ni iko, ban ma isa in kwance maballin takalmansa ba. Shi zai yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.
17 Whose fan is in his hand, and he will thoroughly cleanse his floor, and will gather the wheat into his barn; but the chaff he will burn with fire unquenchable.
Kwaryar shikarsa na hanun sa domin ya share masussukarsa da kyau ya kuma tara alkama a cikin rumbunsa. Amma zai kona buntun da wuta marar mutuwa.
18 And many other things in his exhortation he preached to the people.
Da gargadi masu yawa ya yi wa mutanen wa'azin bishara.
19 But Herod the tetrarch, being reproved by him on account of Herodias his brother Philip’s wife, and for all the evils which Herod had done,
Yahaya kuma ya tsauta wa sarki Hirudus domin ya auri matar dan'uwansa, Hiruduya, da kuma sauran abubuwan da Hirudus ya yi.
20 Added yet this above all, that he shut up John in prison.
Amma Hirudus ya kara yin wani mugun abu. Ya sa an kulle Yahaya a cikin kurkuku.
21 Now when all the people were baptized, it came to pass, that Jesus also being baptized, and praying, the heaven was opened,
Ana nan, lokacin da ake yiwa dukan mutane baftisma, aka yiwa Yesu mai baftisma. Lokacin da yake yin addu'a, sai sama ta bude,
22 And the Holy Spirit descended in a bodily shape like a dove upon him, and a voice came from heaven, which said, Thou art my beloved Son; in thee I am well pleased.
kuma Ruhu Mai Tsarki ya sauko masa a kamanin kurciya, sai wata murya ta fito daga sama, “Kai ne kaunataccen Da na. Ina jin dadin ka.”
23 And Jesus himself began to be about thirty years of age, being ( as was supposed ) the son of Joseph, who was the son of Heli,
Ana nan Yesu da kansa, da ya fara, yana kimanin shekara talatin. Shi dan (kamar yadda ake tsammani) Yusufu ne, dan Heli,
24 Who was the son of Matthat, who was the son of Levi, who was the son of Melchi, who was the son of Janna, who was the son of Joseph,
dan Matat, dan Lawi, dan Malki, dan Yanna, dan Yusufu,
25 Who was the son of Mattathias, who was the son of Amos, who was the son of Nahum, who was the son of Esli, who was the son of Nagge,
dan Matatiya, dan Amos, dan Nahum, dan Hasli, dan Najjaya,
26 Who was the son of Maath, who was the son of Mattathias, who was the son of Semei, who was the son of Joseph, who was the son of Judah,
dan Ma'ata, dan Matatiya, dan Shimeya, dan Yuseka, dan Yoda,
27 Who was the son of Joanna, who was the son of Rhesa, who was the son of Zerubbabel, who was the son of Shealtiel, who was the son of Neri,
dan Yowana, dan Resa, dan Zarubabila, dan Shiyaltiyel, dan Niri,
28 Who was the son of Melchi, who was the son of Addi, who was the son of Cosam, who was the son of Elmodam, who was the son of Er,
dan Malki, dan Addi, dan Kosama, dan Almadama, dan Er,
29 Who was the son of Joshua, who was the son of Eliezer, who was the son of Jorim, who was the son of Matthat, who was the son of Levi,
dan Yosi, dan Aliyeza, dan Yorima, dan Matat, dan Lawi,
30 Who was the son of Simeon, who was the son of Judas, who was the son of Joseph, who was the son of Jonan, who was the son of Eliakim,
dan Saminu, dan Yahuda, dan Yusufu, dan Yonana, dan Aliyakima,
31 Who was the son of Melea, who was the son of Menan, who was the son of Mattatha, who was the son of Nathan, who was the son of David,
dan Malaya, dan Mainana, dan Matata, dan Natan, dan Dauda,
32 Who was the son of Jesse, who was the son of Obed, who was the son of Boaz, who was the son of Salmon, who was the son of Nahshon,
dan Yesse, dan Obida, dan Bu'aza, dan Salmon, dan Nashon,
33 Who was the son of Amminadab, who was the son of Ram, who was the son of Hezron, who was the son of Perez, who was the son of Judah,
dan Amminadab, dan Adimi, dan Arama, dan Hezruna, dan Feresa, dan Yahuda,
34 Who was the son of Jacob, who was the son of Isaac, who was the son of Abraham, who was the son of Terah, who was the son of Nahor,
dan Yakubu, dan Ishaku, dan Ibrahim, dan Tera, dan Nahor,
35 Who was the son of Serug, who was the son of Reu, who was the son of Peleg, who was the son of Eber, who was the son of Shelah,
dan Serug, dan Reyu, dan Feleg, dan Abiru, dan Shela,
36 Who was the son of Cainan, who was the son of Arphaxad, who was the son of Shem, who was the son of Noah, who was the son of Lamech,
dan Kainana, dan Arfakshada, dan Shem, dan Nuhu, dan Lamek,
37 Who was the son of Methuselah, who was the son of Enoch, who was the son of Jared, who was the son of Mahalaleel, who was the son of Cainan,
dan Metusela, dan Anuhu, dan Yaret, dan Mahalel, dan Kainana,
38 Who was the son of Enos, who was the son of Seth, who was the son of Adam, who was the son of God.
dan Enosh, dan Shitu, dan Adamu, dan Allah.

< Luke 3 >