< Job 19 >

1 Then Job answered and said,
Sai Ayuba ya amsa,
2 How long will ye vex my soul, and break me in pieces with words?
“Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
3 These ten times have ye reproached me: ye are not ashamed that ye make yourselves strange to me.
Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
4 And be it indeed that I have erred, my error remaineth with myself.
In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
5 If indeed ye will magnify yourselves against me, and plead against me my reproach:
In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
6 Know now that God hath overthrown me, and hath surrounded me with his net.
sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
7 Behold, I cry out of wrong, but I am not heard: I cry aloud, but there is no judgment.
“Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
8 He hath fenced up my way that I cannot pass, and he hath set darkness in my paths.
Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
9 He hath stripped me of my glory, and taken the crown from my head.
Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
10 He hath destroyed me on every side, and I am gone: and my hope hath he removed like a tree.
Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
11 He hath also kindled his wrath against me, and he counteth me to him as one of his enemies.
Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
12 His troops come together, and raise up their way against me, and encamp around my tent.
Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
13 He hath put my brethren far from me, and my acquaintance are verily estranged from me.
“Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
14 My kinsmen have failed, and my familiar friends have forgotten me.
Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
15 They that dwell in my house, and my maids, count me for a stranger: I am an alien in their sight.
Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
16 I called my servant, and he gave me no answer; I entreated him with my mouth.
Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
17 My breath is strange to my wife, though I make supplication to the children of my own body.
Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
18 Yea, young children despised me; I arose, and they spoke against me.
Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
19 All my close friends abhorred me: and they whom I loved are turned against me.
Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
20 My bone cleaveth to my skin and to my flesh, and I have escaped with the skin of my teeth.
Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
21 Have pity upon me, have pity upon me, O ye my friends; for the hand of God hath touched me.
“Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
22 Why do ye persecute me as God, and are not satisfied with my flesh?
Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
23 O that my words were now written! O that they were printed in a book!
“Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
24 That they were engraved with an iron pen in lead in the rock for ever!
a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
25 For I know that my redeemer liveth, and that he shall stand at the latter day upon the earth:
Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
26 And though after my skin worms destroy this body, yet in my flesh shall I see God:
Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
27 Whom I shall see for myself, and my eyes shall behold, and not another; though my reins be consumed within me.
Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
28 But ye should say, Why persecute we him, seeing the root of the matter is found in me?
“In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
29 Be ye afraid of the sword: for wrath bringeth the punishments of the sword, that ye may know there is a judgment.
sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”

< Job 19 >