< Deuteronomy 6 >

1 Now these are the commandments, the statutes, and the judgments, which the LORD your God commanded to teach you, that ye may do them in the land where ye go to possess it:
Waɗannan su ne umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnku ya umarce ni in koya muku don ku kiyaye a ƙasar da kuke haye Urdun don mallaka,
2 That thou mayest fear the LORD thy God, to keep all his statutes and his commandments, which I command thee, thou, and thy son, and thy son’s son, all the days of thy life; and that thy days may be prolonged.
saboda ku,’ya’yanku, da kuma’ya’yansu bayansu za su ji tsoron Ubangiji Allahnku muddin kuna rayuwa ta wurin kiyaye dukan ƙa’idodinsa da umarnan da na ba ku, da kuma don ku yi tsawon rai.
3 Hear therefore, O Israel, and observe to do it; that it may be well with thee, and that ye may increase mightily, as the LORD God of thy fathers hath promised thee, in the land that floweth with milk and honey.
Ku ji, ya Isra’ila, ku kuma kula, ku kiyaye su don yă zama muku da lafiya, ku kuma ƙaru sosai a ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji, Allahn kakanninku ya yi muku alkawari.
4 Hear, O Israel: The LORD our God is one LORD:
Ku ji, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
5 And thou shalt love the LORD thy God with all thy heart, and with all thy soul, and with all thy might.
Ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku, da dukan ranku, da kuma dukan ƙarfinku.
6 And these words, which I command thee this day, shall be in thy heart:
Waɗannan umarnai da nake ba ku a yau, za su kasance a zukatanku.
7 And thou shalt teach them diligently to thy children, and shalt talk of them when thou sittest in thy house, and when thou walkest by the way, and when thou liest down, and when thou risest up.
Ku koya wa’ya’yanku su da himma. Yi musu magana game da su sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya a hanya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
8 And thou shalt bind them for a sign upon thy hand, and they shall be as frontlets between thy eyes.
Ku ɗaura su su zama alamu a hannuwanku, ku kuma ɗaura su a goshinku.
9 And thou shalt write them upon the posts of thy house, and on thy gates.
Ku rubuta su a dogaran ƙofofin gidajenku, da ƙofofinku.
10 And it shall be, when the LORD thy God shall have brought thee into the land which he swore to thy fathers, to Abraham, to Isaac, and to Jacob, to give thee great and goodly cities, which thou didst not build,
Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da ya rantse ga kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, yă ba ku, ƙasa mai girma, mai manyan biranen da ba ku kuka gina ba,
11 And houses full of all good things, which thou didst not fill, and dug wells, which thou didst not dig, vineyards and olive trees, which thou didst not plant; when thou shalt have eaten and be full;
gidaje cike da kowane irin abubuwa masu kyau, da ba ku kuka tanadar ba, rijiyoyin da ba ku kuka haƙa ba, da gonakin inabi da itatuwan zaitun da ba ku kuka shuka ba, sa’ad da kuwa kuka ci, kuka kuma ƙoshi,
12 Then beware lest thou shouldest forget the LORD, who brought thee forth from the land of Egypt, from the house of bondage.
ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji wanda ya fitar da ku daga Masar, da gidan bauta ba.
13 Thou shalt fear the LORD thy God, and serve him, and shalt swear by his name.
Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku bauta masa shi kaɗai, ku kuma yi alkawaranku da sunansa.
14 Ye shall not go after other gods, of the gods of the people which are around you;
Kada ku bi waɗansu alloli, allolin mutanen da suke kewaye da ku;
15 (For the LORD thy God is a jealous God among you) lest the anger of the LORD thy God should be kindled against thee, and destroy thee from off the face of the earth.
gama Ubangiji Allahnku, wanda yake cikinku, Allah ne mai kishi, fushinsa kuma zai yi ƙuna gāba da ku, zai kuma hallaka ku daga fuskar ƙasar.
16 Ye shall not tempt the LORD your God, as ye tempted him in Massah.
Kada ku gwada Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka yi a Massa.
17 Ye shall diligently keep the commandments of the LORD your God, and his testimonies, and his statutes, which he hath commanded thee.
Ku tabbata kun kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, da farillansa da kuma ƙa’idodinsa da ya ba ku.
18 And thou shalt do that which is right and good in the sight of the LORD: that it may be well with thee, and that thou mayest go in and possess the good land which the LORD swore to thy fathers,
Ku aikata abin da yake daidai da kuma mai kyau a idon Ubangiji, don yă zama muka da lafiya, ku kuwa shiga ku mallaki ƙasa mai kyau da Ubangiji ya yi alkawari da rantsuwa ga kakanninku.
19 To cast out all thy enemies from before thee, as the LORD hath spoken.
Zai kuwa korin dukan abokan gābanku da suke gabanku, yadda Ubangiji ya faɗa.
20 And when thy son shall ask thee in time to come, saying, What mean the testimonies, and the statutes, and the judgments, which the LORD our God hath commanded you?
Nan gaba, sa’ad da’ya’yanku suka tambaye ku, “Mene ne ma’anar farillai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnmu ya umarce ku?”
21 Then thou shalt say to thy son, We were Pharaoh’s slaves in Egypt; and the LORD brought us out of Egypt with a mighty hand:
Sai ku gaya musu, “Dā mu bayin Fir’auna ne a Masar, amma Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu masu ƙarfi.
22 And the LORD showed signs and wonders, great and terrible, upon Egypt, upon Pharaoh, and upon all his household, before our eyes:
A idanunmu Ubangiji ya aikata manyan alamu masu banmamaki, da al’ajabai gāba da Masarawa, da Fir’auna, da kuma dukan gidansa.
23 And he brought us out from there, that he might bring us in, to give us the land which he swore to our fathers.
Amma ya fitar da mu daga can domin yă kawo mu cikin ƙasar da ya yi wa kakanninmu alkawari tare da rantsuwa zai ba mu.
24 And the LORD commanded us to do all these statutes, to fear the LORD our God, for our good always, that he might preserve us alive, as it is at this day.
Ubangiji ya umarce mu mu yi biyayya da dukan waɗannan ƙa’idodi, mu kuma ji tsoron Ubangiji Allahnmu, saboda kullum mu ci gaba, a kuma bar mu da rai, kamar yadda yake a yau.
25 And it shall be our righteousness, if we observe to do all these commandments before the LORD our God, as he hath commanded us.
In kuma muka kula, muka kiyaye dukan dokokin nan a gaban Ubangiji Allahnmu, kamar yadda ya umarce mu, wannan zai zama adalci a gare mu.”

< Deuteronomy 6 >