< Acts 13 >
1 Now there were in the church that was at Antioch certain prophets and teachers; as Barnabas, and Simeon that was called Niger, and Lucius of Cyrene, and Manaen, who had been brought up with Herod the tetrarch, and Saul.
A cikin iklisiyar da take Antakiya, akwai annabawa da malamai. Sune su Barnabas, Saminu (wadda ake kira Baki) da Lukiya Bakurame da Manayin (wanda aka yi renon su tare da sarki Hiridus mai mulki) da Shawulu.
2 As they ministered to the Lord, and fasted, the Holy Spirit said, Separate for me Barnabas and Saul for the work to which I have called them.
Sa'adda suke bauta wa Allah tare da azumi, sai Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Ku kebe mani Barnaba da Shawulu domin aikin da na kiraye su”.
3 And when they had fasted and prayed, and laid their hands on them, they sent them away.
Bayan taron sun yi addu'a da azumi, sai suka sa masu hannu, su suka sallame su.
4 So they, being sent forth by the Holy Spirit, departed to Seleucia; and from there they sailed to Cyprus.
Sai Shawulu da Barnabas suka yi biyayya da Ruhu Mai Tsarki suka tafi Sulukiya; daga nan suka ketare zuwa tsibirin Kuburus.
5 And when they were at Salamis, they preached the word of God in the synagogues of the Jews: and they had also John as their helper.
Sa'adda suke garin Salami, suka koyar da maganar Ubangiji a majami'un Yahudawa, suna kuma tare da Yahaya Markus mai taimakonsu.
6 And when they had gone through the isle to Paphos, they found a certain sorcerer, a false prophet, a Jew, whose name was Barjesus:
Bayan sun zaga tsibirin duka har Bafusa, nan suka iske wani Bayahude mai suna Bar-yeshua mai tsafi kuma annabin karya.
7 Who was with the deputy of the country, Sergius Paulus, a prudent man; who called for Barnabas and Saul, and desired to hear the word of God.
Wannan mai tsafin wanda ke tare da Makaddas, shi Sarjus Bulus mutum mai basira ne. Wannan kuwa ya kira Shawulu da Barnaba domin yana so ya ji maganar Allah.
8 But Elymas the sorcerer ( for so is his name by interpretation ) withstood them, seeking to turn away the deputy from the faith.
Amma Elimas “mai tsafi” (fasarar sunansa kenan) ya yi adawa da su; yana so ya baudar da Makaddashin daga bangaskiya.
9 Then Saul, ( who also is called Paul, ) filled with the Holy Spirit, set his eyes on him,
Amma Shawulu wanda ake ce da shi Bulus yana cike da Ruhu Mai Tsarki ya kafa masa ido.
10 And said, O full of all deceit and all mischief, thou child of the devil, thou enemy of all righteousness, wilt thou not cease to pervert the right ways of the Lord?
Sai ya ce, “Kai dan iblis, kana cike da kowace irin yaudara da mugunta. Kai abokin gabar kowanne irin adalci ne. Ba za ka daina karkata mikakkakun hanyoyin Ubangiji ba?
11 And now, behold, the hand of the Lord is upon thee, and thou shalt be blind, not seeing the sun for a season. And immediately there fell on him a mist and a darkness; and he went about seeking some to lead him by the hand.
Yanzu ga hannun Ubangiji bisa kanka, zaka zama makaho. Ba za ka ga rana ba nan da dan lokaci.” Nan take kuwa sai wani hazo da duhu suka rufe shi ya fara yawo yana neman mutane su yi masa jagora.
12 Then the deputy, when he saw what was done, believed, being astonished at the doctrine of the Lord.
Bayan da Makaddashin ya ga abin da ya faru ya ba da gaskiya saboda ya yi mamakin koyarwa game da Ubangiji.
13 Now when Paul and his company loosed from Paphos, they came to Perga in Pamphylia: and John departing from them returned to Jerusalem.
Bulus da abokansa suka shirya suka ketare a jirgin ruwa daga Bafusa zuwa Firjiya a Bamfiliya. Amma Yahaya ya bar su ya koma Urushalima.
14 But when they departed from Perga, they came to Antioch in Pisidia, and went into the synagogue on the sabbath day, and sat down.
Bulus da abokansa suka tafi daga Firjiya zuwa Antakiya na kasar Bisidiya. Nan suka shiga majami'a ran Asabaci suka zauna.
15 And after the reading of the law and the prophets the rulers of the synagogue sent to them, saying, Men, brethren, if ye have any word of exhortation for the people, say on.
Bayan karatun dokoki da annabawa, shugabanin iklisiyar suka tura sako cewa, “'Yan'uwa, idan kuna da wani sakon karfafawa ga jama'a ku fadi.”
16 Then Paul stood up, and beckoning with his hand said, Men of Israel, and ye that fear God, listen.
Bulus kuwa ya tashi ya yi alama da hannunsa ya ce, “Mutanen Isra'ila da ku wadanda kuke girmama Allah, ku ji.
17 The God of this people Israel chose our fathers, and exalted the people when they dwelt as strangers in the land of Egypt, and with an high arm he brought them out of it.
Allahn Isar'ila ya zabi kakkaninmu ya kuma ribabbanya su sa'adda suke kasar Masar da kuma madaukakin iko ya fito da su daga cikinta.
18 And about the time of forty years he bore their manners in the wilderness.
Ya yi hakuri da su a jeji har na tsawon shekara arba'in.
19 And when he had destroyed seven nations in the land of Canaan, he divided their land to them by lot.
Bayan ya hallaka kasashe bakwai a kasar Kan'ana, ya ba kakkaninmu kasar nan gado.
20 And after these things, which took about four hundred and fifty years, he gave to them judges, until Samuel the prophet.
Duk wadanan abubuwan sun faru shekaru dari hudu da hamsin da suka wuce. Bayan wadannan, Allah ya ba su alkalai har sai da annabi Sama'ila ya zo.
21 And afterward they desired a king: and God gave to them Saul the son of Kish, a man of the tribe of Benjamin, by the space of forty years.
Sai jama'a suka roka a ba su sarki, Allah kuwa ya ba su Saul dan Kish, mutumin kabilar Binyamin ya zama sarki har na tsawon shekara arba'in.
22 And when he had removed him, he raised up to them David to be their king; to whom also he gave testimony, and said, I have found David the son of Jesse, a man after my own heart, who shall fulfil all my will.
Allah kuwa ya cire shi daga kan kujerar sarauta, ya daga Dauda ya zama sarkinsu. A kan Dauda ne Allah ya ce, 'Na sami Dauda dan Yessi, mutumin da zuciyata ke so; zai yi duk abin da nake so'.
23 Of this man’s seed hath God according to his promise raised up to Israel a Saviour, Jesus:
Daga zuriyar mutumin nan Allah ya fito da mai ceto, Yesu, kamar yadda aka alkawarta zai yi.
24 After John had first preached before his coming the baptism of repentance to all the people of Israel.
Wannan ya faru kafin Yesu ya zo, Yahaya ya yi shelar baftimar tuba ga jamma'ar Isra'ila.
25 And as John fulfilled his course, he said, Whom think ye that I am? I am not he. But, behold, there cometh one after me, whose shoes of his feet I am not worthy to loose.
Sa'adda Yahaya ya gama aikin sa, sai ya ce, 'Wanene ni a tsamanin ku? Ba nine shi ba. Amma ku saurara, akwai wani mai zuwa bayana wanda maballin takalminsa ban isa in kwance ba.'
26 Men, brethren, children of the stock of Abraham, and whoever among you feareth God, to you is the word of this salvation sent.
Yan'uwa 'ya'ya daga zuriyar Ibrahim, da wadanda ke bautar Allah a cikinku, saboda mune aka turo sakon ceto.
27 For they that dwell at Jerusalem, and their rulers, because they knew him not, nor yet the words of the prophets which are read every sabbath, they have fulfilled them in condemning him.
Saboda wadanda ke zaune cikin Urushalima, da masu mulkinsu, ba su gane shi ba, kuma sun cika fadin annabawa da a ke karantawa kowace ranar Asabaci ta wurin kashe shi.
28 And though they found no cause of death in him, yet they desired Pilate that he should be put to death.
Duk da cewa ba su sami dalilin mutuwa a kansa ba, suka roki Bilatus ya kashe shi.
29 And when they had fulfilled all that was written concerning him, they took him down from the tree, and laid him in a sepulchre.
Bayan sun gama duk abin da aka rubuta game da shi, sai suka sauke shi daga giciye suka sa shi a cikin kabari.
30 But God raised him from the dead:
Amma Allah ya tashe shi daga matattu.
31 And he was seen many days by them who came up with him from Galilee to Jerusalem, who are his witnesses to the people.
Mutanen da suka zo tare da shi daga Galili da Urushalima kuwa suka yi ta ganinsa har kwanaki da yawa. Wadanan mutane kuma sune shaidunsa ga jama'a a yanzu.
32 And we declare to you the glad tidings, that the promise which was made to the fathers,
Mun kawo maku labari mai dadi game da alkawaran da aka yi wa kakkaninmu.
33 God hath fulfilled the same to us their children, in that he hath raised up Jesus again; as it is also written in the second psalm, Thou art my Son, this day have I begotten thee.
Ubangiji ya bar mana alkawaran. Don haka ya ta da Yesu daga matattu. Kamar yadda ya ke a littafin zabura ta biyu: ''Kai da na ne yau na zama mahaifinka.''
34 And as concerning that he raised him from the dead, now no more to return to corruption, he said in this way, I will give you the sure mercies of David.
Kuma dalilin tayar da shi daga matattu shine saboda kada jikinsa ya rube, ya yi magana kamar haka: ''Zan baku albarkun Dauda masu tsarki tabatattu.''
35 Therefore he saith also in another psalm, Thou shalt not allow thy Holy One to see corruption.
Wannan shine dalilin da ya yi magana kuma a wata Zabura, 'Ba za ka bar Mai Tsarkinka ya rube ba.'
36 For David, after he had served his own generation by the will of God, fell asleep, and was laid to his fathers, and saw corruption:
Bayan Dawuda ya yi wa Allah bauta a cikin zuciyarsa da kuma abin da Allah yake so, ya mutu, aka binne shi tare da kakkaninsa, ya kuma ruba,
37 But he, whom God raised again, saw no corruption.
amma wanda Allah ya tayar bai ga ruba ba.
38 Be it known to you therefore, men, brethren, that through this man is preached to you the forgiveness of sins:
'Yan'uwa, ku sani cewa ta wurin mutumin nan aka yi maku wa'azin gafarar zunubai.
39 And by him all that believe are justified from all things, from which ye could not be justified by the law of Moses.
Ta wurinsa ne duk wanda ya ba da gaskiya zai kubuta daga dukan abin da dokar Musa bata 'yantar da ku a kai ba.
40 Beware therefore, lest that come upon you, which is spoken in the prophets;
Saboda haka ku yi hankali da abubuwan da annabawa suka fada kada su faru a kanku:
41 Behold, ye despisers, and wonder, and perish: for I work a work in your days, a work which ye shall by no means believe, though a man declare it to you.
'Ku masu reni, za ku rude don mamaki, ku kuma shude; saboda ina aiki a cikin kwananakinku, aikin da ba za ku yarda ba ko da wani ya gaya maku.”
42 And when the Jews had gone out of the synagogue, the Gentiles besought that these words might be preached to them the next sabbath.
Da Bulus da Barnaba suna fita kenan, sai jama'a suka rokesu, su sake yin irin wannan magana ranar Assabaci mai zuwa.
43 Now when the congregation was broken up, many of the Jews and religious proselytes followed Paul and Barnabas: who, speaking to them, persuaded them to continue in the grace of God.
Bayan da sujadar ta kare, Yahudawa da yawa da kuma wadanda suka shiga addinin Yahudanci suka bi Bulus da Barnaba, sai suka gargade su da su cigaba da aikin alherin Allah.
44 And the next sabbath came almost the whole city together to hear the word of God.
Da Asabaci ta kewayo, kusan dukan garin suka taru domin su ji maganar Ubangiji.
45 But when the Jews saw the multitudes, they were filled with envy, and spoke against those things which were spoken by Paul, contradicting and blaspheming.
Sa'adda Yahudawa suka ga taron jama'a, sai suka cika da kishi suna karyata abubuwan da Bulus ya fada suka kuma aibata shi.
46 Then Paul and Barnabas became bold, and said, It was necessary that the word of God should first be spoken to you: but seeing ye reject it, and judge yourselves unworthy of everlasting life, lo, we turn to the Gentiles. (aiōnios )
Amma Bulus da Barnaba sun yi magana gabagadi suka ce, “Dole ne a fara fada maku maganar Allah. Amma da yake kun ture ta, kun nuna baku cancanci rai madawwami ba soboda haka zamu juya ga al'ummai. (aiōnios )
47 For so hath the Lord commanded us, saying, I have set thee to be a light of the Gentiles, that thou shouldest be for salvation to the ends of the earth.
Don haka Ubangiji ya umarce mu, cewa, 'Na sa ku haske ga al'ummai, saboda ku kawo ceto ga iyakar duniya.'”
48 And when the Gentiles heard this, they were glad, and glorified the word of the Lord: and as many as were ordained to eternal life believed. (aiōnios )
Da al'ummai suka ji haka, sai suka yi murna suka kuma yabi kalmar Ubangiji. Dukan wadanda aka kaddarawa samin rai madawwami suka tuba. (aiōnios )
49 And the word of the Lord was proclaimed throughout all the region.
Kalmar Ubangiji kuwa ta bazu a kowanne bangaren yankin.
50 But the Jews stirred up the devout and honourable women, and the chief men of the city, and raised persecution against Paul and Barnabas, and drove them out of their land.
Amma Yahudawan suka zuga wadansu mata masu sujada, masu daraja da kuma shugabannin mazan garin. Wannan ya tayar da tsanani ga Bulus da Barnaba har suka fitar da su daga iyakar garinsu.
51 But they shook off the dust of their feet against them, and came to Iconium.
Amma Bulus da Barnaba suka kade masu kurar kafarsu. Suka tafi garin Ikoniya.
52 And the disciples were filled with joy, and with the Holy Spirit.
Amma almajiran suka cika da farin ciki da kuma Ruhu Mai Tsarki.