< Zechariah 9 >
1 “This is a declaration of Yahweh's word concerning the land of Hadrak and Damascus, its resting place; for the eyes of all humanity and all the tribes of Israel are toward Yahweh.
Annabci. Maganar Ubangiji tana gāba da ƙasar Hadrak za tă kuma sauko a kan Damaskus, gama idanun dukan mutane da na kabilan Isra’ila suna a kan Ubangiji,
2 This declaration also concerns Hamath, which borders on Damascus, and it concerns Tyre and Sidon, for they are very wise.
da kuma a kan Hamat ita ma, wadda ta yi iyaka da ita, da kuma a kan Taya da Sidon, ko da yake suna da hikima ƙwarai.
3 Tyre has built herself a stronghold and heaped up silver like dust and refined gold like mud in the streets.
Taya ta gina wa kanta mafaka mai ƙarfi; ta tara azurfa kamar ƙasa, zinariya kuma kamar tarin shara a tituna.
4 Look! The Lord will dispossess her and destroy her strength on the sea, so she will be devoured by fire.
Amma Ubangiji zai karɓe mallakarta, zai hallaka ikonta da take da shi a kan teku, wuta kuma za tă cinye ta.
5 Ashkelon will see and be afraid! Gaza also will tremble greatly! Ekron, her hopes will be disappointed! The king will perish from Gaza, and Ashkelon shall no longer be inhabited!
Ashkelon za tă ga haka ta ji tsoro; Gaza za tă yi birgima cikin azaba, haka Ekron ma, gama za tă fid da zuciya. Gaza za tă rasa sarkinta za a kuma gudu a bar Ashkelon.
6 Strangers will make their homes in Ashdod, and I will cut off the pride of the Philistines.
Baƙi za su mallaki Ashdod, kuma zan kawar da girman kan Filistiyawa.
7 For I will remove their blood from their mouths and their abominations from between their teeth. Then they will become a remnant for our God like a clan in Judah, and Ekron will become like the Jebusites.
Zan kawar da jini daga bakinsu, zan kuma cire abincin da aka haramta daga tsakanin haƙoransu. Waɗanda za a bari za su zama na Allahnmu, su kuma zama shugabanni a Yahuda, Ekron kuma za tă zama kamar Yebusiyawa.
8 I will camp around my land against enemy armies, so no one can pass through or return, for no oppressor will overrun them, for now I see with my own eyes!
Amma zan kāre gidana daga sojoji masu kai da kawowa. Azzalumi ba zai ƙara cin mutanena da yaƙi ba, gama yanzu ina tsaro.
9 Shout with great joy, daughter of Zion! Shout with happiness, daughter of Jerusalem! Behold! Your king is coming to you with righteousness and is rescuing you. He is humble and is riding on a donkey, on the colt of a donkey.
Ki yi murna ƙwarai, ya Diyar Urushalima! Ki yi sowa, Diyar Urushalima! Duba, ga sarkinki yana zuwa wurinki, mai adalci yana kuma da ceto, mai tawali’u yana kuma hawan jaki, yana a kan ɗan aholaki, a kan’yar jaka.
10 Then I will cut off the chariot from Ephraim and the horse from Jerusalem, and the bow will be cut off from battle; for he will speak peace to the nations, and his dominion will be from sea to sea, and from the River to the ends of the earth!
Zan ƙwace kekunan yaƙi daga Efraim, da kuma dawakan yaƙi daga Urushalima, za a kuma karya bakan yaƙi. Zai yi shelar salama ga al’ummai. Mulkinsa zai yaɗu daga teku zuwa teku, daga Kogi kuma zuwa ƙarshen duniya.
11 As for you, because of the blood of my covenant with you, I will set your prisoners free from the pit where there is no water.
Ke kuma, saboda jinin alkawarina da ke, zan’yantar da’yan kurkukunki daga rami marar ruwa.
12 Return to the stronghold, prisoners of hope! Even today I am declaring that I will return double to you,
Ku koma maɓuya, ya ku’yan kurkuku masu sa zuciya; ko yanzu ma na sanar cewa zan mayar muku ninki biyu.
13 for I have bent Judah as my bow. I have filled my quiver with Ephraim. I have roused your sons, Zion, against your sons, Greece, and have made you, Zion, like a warrior's sword!”
Zan lanƙwasa Yahuda yadda nake lanƙwasa bakana, in kuma cika ta da Efraim kamar kibiya. Zan tā da’ya’yanki maza, ya Sihiyona, gāba da’ya’yanki, ya Girka, in kuma mai da ke kamar takobin jarumin yaƙi.
14 Yahweh will appear to them, and his arrows will shoot out like lightning! For my Lord Yahweh will blow the trumpet and will advance with the storms from Teman.
Sa’an nan Ubangiji zai bayyana a bisansu; kibiyarsa za tă wulga kamar walƙiya. Ubangiji Mai Iko Duka zai busa ƙaho; zai taho ta cikin guguwa daga kudu,
15 Yahweh of hosts will defend them, and they will devour them and defeat the stones of the slings. Then they will drink and shout like men drunk on wine, and they will be filled with wine like bowls, like the corners of the altar.
Ubangiji Maɗaukaki kuma zai tsare su. Za su hallakar su kuma yi nasara da duwatsun majajjawa. Za su sha su yi kururuwa kamar sun sha ruwan inabi; za su cika kamar kwanon da ake amfani don a yayyafa jini a kusurwoyin bagade.
16 So Yahweh their God will rescue them on that day, as the flock of his people. They are the jewels of a crown that will shine on his land.
Ubangiji Allahnsu zai cece su a wannan rana gama su mutanensa ne da kuma garkensa. Za su haska a cikin ƙasarsa kamar lu’ulu’u a rawani.
17 How good and how beautiful they will be! The young men will flourish on grain and the virgins on sweet wine!”
Za su yi kyan gani da kuma bansha’awa! Hatsi zai sa samari su yi murna, sabon ruwan inabi kuma zai sa’yan mata su yi farin ciki.