< Zechariah 11 >
1 Open your doors, Lebanon, that fire may devour your cedars!
Buɗe ƙofofinki, ya Lebanon, don wuta ta cinye itatuwan al’ul naki.
2 Lament, cypress trees, for the cedar trees have fallen! What was majestic has been devastated! Lament, you oaks of Bashan, for the strong forest has gone down.
Yi kuka, ya itacen fir, gama itacen al’ul ya fāɗi; itatuwa masu daraja sun lalace! Ku yi kuka, ku itatuwan oak na Bashan; an sassare itatuwan babban kurmi!
3 The shepherds howl, for their glory has been destroyed! The voice of the young lions' roar, for the pride of the Jordan River has been devastated!
Ku ji kukan makiyaya; an ɓata musu wuraren kiwonsu masu ciyayi! Ku ji rurin zakoki; an lalatar da jejin Urdun!
4 This is what Yahweh my God says, “Like a shepherd, watch over the flock set aside for slaughter!
Ga abin da Ubangiji Allahna ya ce, “Yi kiwon garken tumakin da za a yanka.
5 (The ones who buy them slaughter them and are not punished, and the ones who sell them say, 'Blessed be Yahweh! I have become rich!' for the shepherds working for the flocks' owners have no pity on them.)
Masu sayensu sun yanyanka su, suka kuwa tafi ba hukunci. Masu sayar da su sun ce, ‘Yabi Ubangiji, na yi arziki!’ Makiyayansu ma ba su ji tausayinsu ba.
6 For I will no longer pity the inhabitants of the land!—this is Yahweh's declaration. See! I myself am about to turn over every person into the hand of his neighbor and into the hand of his king, and they will destroy the land and none of them will I deliver them from their hand.”
Gama ba zan ƙara jin tausayin mutanen ƙasar ba,” in ji Ubangiji. “Zan ba da kowa ga maƙwabcinsa da kuma sarkinsa. Za su zalunci ƙasar, ba zan kuma cece su daga hannuwansu ba.”
7 So I became the shepherd of the flock marked for slaughter, for those who dealt in sheep. I took two staffs; one staff I called “Favor” and the other I called “Unity.” In this way I shepherded the flock.
Saboda haka na yi kiwon garken da za a yanka, musamman garken da ake zalunta. Sai na ɗauki sanduna biyu na kira ɗaya Tagomashi, ɗaya kuma Haɗinkai, sai na yi kiwon garken.
8 In one month I destroyed the three shepherds. I became impatient with them, and they also hated me.
Cikin wata guda na kawar da makiyayan nan uku. Garken suka ƙi ni, na kuwa gaji da su
9 Then I said to the owners, “I will not work as a shepherd for you any longer. The sheep that are dying—let them die; the sheep that are being destroyed—let them be destroyed. Let the sheep that remain each eat the flesh of its neighbor.”
na ce, “Ba zan zama makiyayinku ba. Bari masu mutuwa su mutu, masu hallaka kuma su hallaka. Bari waɗanda suka ragu su ci naman juna.”
10 So I took my staff “Favor” and broke it to break the covenant that I had made with all of my tribes.
Sai na ɗauki sandana mai suna Tagomashi na karya shi, na janye alkawarin da na yi da dukan al’ummai.
11 On that day the covenant was broken, and those who dealt in sheep and who were watching me knew that Yahweh had spoken.
An janye shi a ranan nan, saboda haka garken da yake cikin wahala masu kallona sun san cewa maganar Ubangiji ce.
12 I said to them, “If it seems good to you, pay me my wages. But if not, do not do it.” So they weighed out my wages—thirty pieces of silver.
Na faɗa musu cewa, “In kun ga ya fi kyau, ku biya ni; in kuwa ba haka ba, ku riƙe.” Saboda haka suka biya ni azurfa talatin.
13 Then Yahweh said to me, “Deposit the silver in the treasury, the excellent price at which they valued you!” So I took the thirty pieces of silver and deposited them in the treasury in the house of Yahweh.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Jefar da shi cikin ma’aji,” Lada mai kyau da aka yi cinikina ne! Saboda haka sai na ɗauki azurfa talatin ɗin na jefa su cikin gidan Ubangiji don a sa cikin ma’aji.
14 Then I broke my second staff, “Unity,” to break the brotherhood between Judah and Israel.
Sai na karya sandana na biyu mai suna Haɗinkai, ta haka na karya’yan’uwantakar da take tsakanin Yahuda da Isra’ila.
15 Yahweh said to me, “Again, take the equipment of a foolish shepherd for yourself,
Sai Ubangiji ya ce mini, “Ka sāke ɗaukar kayan aiki na wawan makiyayi.
16 for see, I am about to set in place a shepherd in the land. He will not care for the perishing sheep. He will not seek out the sheep gone missing, nor heal the crippled sheep. He will not feed the sheep that are healthy, but will eat the flesh of the fattened sheep and will tear off their hooves.
Gama zan tā da makiyayi a ƙasar wanda ba zai kula da ɓatattu, ko yă nemi ƙanana, ko yă warkar da waɗanda suka ji ciwo, ko kuma ciyar da masu lafiya ba, sai dai zai ci naman keɓaɓɓun tumaki, yă farfasa kofatonsu.
17 Woe to the worthless shepherd who forsakes the flock! May the sword come against his arm and his right eye! May his arm wither away and may his right eye become blind!”
“Kaito ga banzan makiyayin nan, wanda ya bar garken! Bari takobi yă sare hannunsa da idonsa na dama! Bari hannunsa yă shanye gaba ƙaf, idonsa na dama kuma yă makance sarai!”