< Revelation 21 >

1 Then I saw a new heaven and a new earth, for the first heaven and the first earth had passed away, and the sea was no more.
Sai na ga sabuwar sama da sabuwar duniya, domin sama ta fari da duniya ta fari sun shude, ba kuma teku.
2 I saw the holy city, new Jerusalem, that came down out of heaven from God, prepared like a bride adorned for her husband.
Na ga birni mai tsarki, sabuwar Urushalima, wadda ta sauko kasa daga sama wurin Allah, shiryayya kamar amaryar da aka yi wa ado domin mijinta.
3 I heard a great voice from the throne saying, “Look! The dwelling place of God is with human beings, and he will live with them. They will be his people, and God himself will be with them and he will be their God.
Na ji babbar murya daga kursiyinta na cewa, “Duba! Mazaunin Allah yana tare da 'yan adam, zai zauna tare da su. Za su zama mutanensa, Allah kuma da kansa zai kasance tare da su ya kuma zama Allahnsu.
4 He will wipe away every tear from their eyes, and there will be no more death, or grieving, or crying, or pain. The former things have passed away.
Zai share dukan hawaye daga idanunsu, kuma babu sauran mutuwa, ko bakinciki, ko kuka, ko azaba. Abubuwan da sun shude.
5 The one who was seated on the throne said, “Look! I make all things new.” He said, “Write this down because these words are trustworthy and true.”
Shi wanda yake zaune a kan kursiyin ya ce, “Duba! Na maida kome ya zama sabo.” Ya ce, “Ka rubuta wannan domin wadannan kalmomi amintattu ne da gaskiya”.
6 He said to me, “These things are done! I am the alpha and the omega, the beginning and the end. To the one who thirsts I will give drink without cost from the spring of the water of life.
Ya ce mani, “Wadannan abubuwan an gama! Ni ne Alpha da Omega, farko da karshe. Ga mai jin kishi, zan bashi kyauta daga mabulbular ruwan rai.
7 The one who conquers will inherit these things, and I will be his God, and he will be my son.
Wanda ya ci nasara, zai gaji wadannan abubuwa, ni kuma zan zama Allahnsa, shi kuma ya zama da na.
8 But as for the cowards, the faithless, the detestable, the murderers, the sexually immoral, sorcerers, idolaters, and all liars, their place will be in the fiery lake of burning sulfur. That is the second death.” (Limnē Pyr g3041 g4442)
Amma ga matsorata, da marasa bangaskiya, da masu kazanta, da masu kisan kai, da fasikai, da masu sihiri, da masu bautar gumaka, da dukan makaryata, mazaunin su zai kasance cikin tafki mai ci da farar wuta. Mutuwa ta biyu kenan.” (Limnē Pyr g3041 g4442)
9 One of the seven angels came to me, the one who had the seven bowls full of the seven last plagues, and he said, “Come here. I will show you the bride, the wife of the Lamb.”
Daya daga cikin mala'ikun bakwai ya zo wurina, wanda yake dauke da tasoshi bakwai cike da annobai bakwai na karshe, yace, “Zo nan. Zan nuna maka amarya, matar Dan Rago”.
10 Then he carried me away in the Spirit to a great and high mountain and showed me the holy city Jerusalem coming down out of heaven from God.
Sai ya dauke ni cikin Ruhu zuwa wani babban dutse mai tsawo ya nuna mani birni mai-tsarki, Urushalima, tana saukowa daga cikin sama daga wurin Allah.
11 Jerusalem had the glory of God, and its brilliance was like a very precious jewel, like a stone of crystal-clear jasper.
Urushalima tana da daukakar Allah, shekinta yana kama da dutse mai tamani, sai kace dutsen yasfa, garau kamar karau.
12 It had a great, high wall with twelve gates, with twelve angels at the gates. On the gates were written the names of the twelve tribes of the children of Israel.
Tana da babban garu mai tsawo, da kofofi goma sha biyu, da mala'iku goma sha biyu a kofofin. Akan kofofin an rubuta sunayen kabilu sha biyu na 'ya'yan Isra'ila.
13 On the east were three gates, on the north three gates, on the south three gates, and on the west three gates.
A gabas akwai kofofi uku, a arewa kofofi uku, a kudu kofofi uku, da kuma yamma kofofi uku.
14 The wall of the city had twelve foundations, and on them were the twelve names of the twelve apostles of the Lamb.
Garun birnin yana da harsashin gini goma sha biyu, a bisansu akwai sunaye goma sha biyu na manzanni goma sha biyu na Dan Rago.
15 The one who spoke with me had a measuring rod made of gold to measure the city, its gates, and its wall.
Shi wanda yayi magana dani yana da sandan awo na zinariya domin ya auna birnin, da kofofinsa, da garunsa.
16 The city was laid out in a square; its length was the same as its width. He measured the city with the measuring rod, twelve thousand stadia in length (its length, width, and height were the same).
Birnin; da tsawonsa da fadinsa iri daya ne. Ya gwada birnin da sandar awo, mil dubu sha biyu a tsaye (fadinsa, da tsawonsa, da tsayinsa duka daya ne)
17 He also measured its wall, 144 cubits thick by human measurement (which is also the angel's measure).
Ya kuma gwada garunsa, kamu 144, bisa ga gwajin 'yan adam (wanda shine ma'aunin mala'ika).
18 The wall was built of jasper and the city of pure gold, like clear glass.
An gina garun da Yasfa birnin kuma da sahihiyar zinariya, mai kama da madubi mai kyalli.
19 The foundations of the wall were adorned with every kind of precious stone. The first was jasper, the second was sapphire, the third was agate, the fourth was emerald,
An kawata harsashin garun da kowanne irin dutse mai tamani. Na fari yasfa, na biyu saffir, na uku agat, na hudu emerald,
20 the fifth was onyx, the sixth was carnelian, the seventh was chrysolite, the eighth was beryl, the ninth was topaz, the tenth was chrysoprase, the eleventh was jacinth, and the twelfth was amethyst.
na biyar Onis, na shida sardiyus, na bakwai kirisolat, na takwas beril, na tara tofaz, na goma kirisofaras, na sha daya yakinta, na sha biyu kuma ametis.
21 The twelve gates were twelve pearls; each of the gates was made from a single pearl. The streets of the city were pure gold, like transparent glass.
Kofofi goma sha biyu lu'u-lu'ai ne goma sha biyu; kowacce daya a cikin kofofin daga lu'u-lu'u daya aka yi shi. Titunan birnin kuwa zinariya ce sahihiya, sai kace madubi garau.
22 I saw no temple in the city, for the Lord God Almighty and the Lamb are its temple.
Ban ga haikali a cikin birnin ba, gama Ubangiji Allah Mai iko duka da Dan Ragon su ne haikalinsa.
23 The city had no need of the sun or the moon in order to shine on it because the glory of God shone on it, and its lamp is the Lamb.
Birnin ba ya bukatar rana ko wata su haskaka shi gama daukakar Allah ta haskaka shi, kuma fitilarsa Dan Rago ne.
24 The nations will walk by the light of that city. The kings of the earth will bring their splendor into it.
Al'ummai za su yi tafiya cikin hasken birnin. Sarakunan duniya kuma za su kawo daukakarsu cikinsa.
25 Its gates will not be shut during the day, and there will be no night there.
Kofofinsu kuma ba za a rufe su da rana ba, babu dare kuma a can.
26 They will bring the splendor and the honor of the nations into it,
Za su kawo daukaka da darajar al'ummai a cikinsa,
27 but nothing unclean will ever enter into it, nor anyone who does what is shameful or deceitful, but only those whose names are written in the Lamb's Book of Life.
babu wani abu mai kazanta da zai taba shiga cikinsa. Ko wanda yake aikata abin kunya da karya, sai wadanda an rubuta sunayensu a cikin littafin rai na Dan Rago kadai.

< Revelation 21 >