< Psalms 95 >

1 Oh come, let us sing to Yahweh; let us sing joyfully to the rock of our salvation.
Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
2 Let us enter his presence with thanksgiving; let us sing to him with psalms of praise.
Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
3 For Yahweh is a great God and a great King superior to all gods.
Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
4 In his hand are the depths of the earth; the heights of the mountains are his.
A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
5 The sea is his, for he made it, and his hands formed the dry land.
Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
6 Oh come, let us worship and bow down; let us kneel before Yahweh, our Creator:
Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
7 For he is our God, and we are the people of his pasture and the sheep of his hand. Today—oh, that you would hear his voice!
gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
8 “Do not harden your heart, as at Meribah, or as on the day of Massah in the wilderness,
“Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
9 where your forefathers tested me and tried me, though they had seen my deeds.
inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
10 For forty years I was angry with that generation and said, 'This is a people whose hearts wander astray; they have not known my ways.'
Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
11 Therefore I vowed in my anger that they would never enter into my resting place.”
Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”

< Psalms 95 >