< Psalms 77 >
1 For the chief musician; after the manner of Jeduthun. A psalm of Asaph. I will call out with my voice to God; I will call with my voice to God, and my God will hear me.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
2 In the day of my trouble I sought the Lord; at night I stretched my hands out, and they would not become tired. My soul refused to be comforted.
Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
3 I thought of God as I groaned; I thought about him as I grew faint. (Selah)
Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
4 You held my eyes open; I was too troubled to speak.
ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
5 I thought about the days of old, about times long past.
Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
6 During the night I called to mind the song I once sang. I thought carefully and tried to understand what had happened.
na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
7 Will the Lord reject me forever? Will he never again show me favor?
“Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
8 Was his covenant faithfulness gone forever? Had his promise failed forever?
Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
9 Had God forgotten to be gracious? Had his anger shut off his compassion? (Selah)
Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
10 I said, “This is my sorrow: the changing of the right hand of the Most High toward us.”
Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
11 But I will call to mind your deeds, Yahweh; I will think about your wonderful deeds of old.
Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
12 I will ponder all your deeds and will reflect on them.
Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
13 Your way, God, is holy; what god compares to our great God?
Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
14 You are the God who does wonders; you have revealed your strength among the peoples.
Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
15 You gave your people victory by your great power— the descendants of Jacob and Joseph. (Selah)
Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
16 The waters saw you, God; the waters saw you, and they were afraid; the depths trembled.
Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
17 The clouds poured down water; the cloudy skies gave voice; your arrows flew about.
Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
18 Your thunderous voice was heard in the wind; the lightning lit up the world; the earth trembled and shook.
Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
19 Your path went through the sea and your way through the surging waters, but your footprints were not seen.
Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
20 You led your people like a flock by the hand of Moses and Aaron.
Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.