< Psalms 66 >
1 For the chief musician. A song, a psalm. Make a joyful noise to God, all the earth;
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 Sing out the glory of his name; make his praise glorious.
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 Say to God, “How terrifying are your deeds! By the greatness of your power your enemies will submit to you.
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 All the earth will worship you and will sing to you; they will sing to your name.” (Selah)
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
5 Come and see the works of God; he is fearsome in his deeds toward the sons of mankind.
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6 He turned the sea into dry land; they went through the river on foot; there we rejoiced in him.
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7 He rules forever by his might; his eyes observe the nations; let not the rebellious exalt themselves. (Selah)
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
8 Give blessing to God, you people, let the sound of his praise be heard.
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9 He keeps us among the living, and he does not permit our feet to slip.
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10 For you, God, have tested us; you have tested us as silver is tested.
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11 You brought us into a net; you laid a heavy burden on our backs.
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12 You made people ride over our heads; we went through fire and water, but you brought us out into a spacious place.
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
13 I will come into your house with burnt offerings; I will pay you my vows
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14 which my lips promised and my mouth spoke when I was in distress.
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15 I will offer to you burnt offerings of fat animals with the sweet aroma of rams; I will offer bulls and goats. (Selah)
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
16 Come and listen, all you who fear God, and I will declare what he has done for my soul.
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17 I cried to him with my mouth, and he was praised with my tongue.
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18 If I had seen sin within my heart, the Lord would not have listened to me.
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19 But God has truly heard; he has paid attention to the voice of my prayer.
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20 Blessed be God, who has not turned away my prayer or his covenant faithfulness from me.
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!