< Psalms 55 >

1 For the chief musician; on stringed instruments. A maschil of David. Give ear to my prayer, God; and do not hide yourself from my plea.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
2 Pay attention to me and answer me; I have no rest in my troubles
ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
3 because of the voice of my enemies, because of the oppression of the wicked; for they bring trouble on me and persecute me in anger.
hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
4 My heart trembles within me, and the terrors of death have fallen on me.
Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
5 Fearfulness and trembling have come on me, and horror has overwhelmed me.
Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
6 I said, “Oh, if only I had wings like a dove! Then would I fly away and be at rest.
Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
7 See, then I would wander far away; I would stay in the wilderness. (Selah)
da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
8 I would hurry to a shelter from the stormy wind and tempest.”
da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
9 Devour them, Lord, confuse their language! For I have seen violence and strife in the city.
Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
10 Day and night they go about on its walls; iniquity and mischief are in the middle of it.
Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
11 Wickedness is in the middle of it; oppression and deceit do not leave its streets.
Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
12 For it was not an enemy who rebuked me, then I could have borne it; neither was it he who hated me who raised himself up against me, then I would have hidden myself from him.
Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
13 But it was you, a man equal to myself, my companion and my close friend.
Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
14 We had sweet fellowship together; we walked in the house of God with the throng.
wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
15 Let death come suddenly on them; let them go down alive to Sheol, for wickedness is where they live, right among them. (Sheol h7585)
Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol h7585)
16 As for me, I will call on God, and Yahweh will save me.
Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
17 In the evening, morning and at noonday I complain and moan; he will hear my voice.
Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
18 He will safely rescue my life from the battle that was against me, for those who fought against me were many.
Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
19 God, the one who rules from eternity, will hear them and humiliate them. (Selah) They never change, and they do not fear God.
Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
20 My friend has raised his hands against those who were at peace with him; he has not respected the covenant that he had.
Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
21 His mouth was smooth as butter, but his heart was hostile; his words were softer than oil, yet they were actually drawn swords.
Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
22 Place your burdens on Yahweh, and he will sustain you; he will never allow a righteous person to totter.
Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
23 But you, God, will bring the wicked down into the pit of destruction; bloodthirsty and deceitful men will not live even half as long as others, but I will trust in you.
Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.

< Psalms 55 >