< Psalms 3 >
1 A psalm of David, when he fled from Absalom his son. Yahweh, how many are my enemies! Many have risen against me.
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
2 Many say about me, “There is no help for him from God.” (Selah)
Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
3 But you, Yahweh, are a shield around me, my glory, and the one who lifts up my head.
Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
4 I lift up my voice to Yahweh, and he answers me from his holy hill. (Selah)
Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
5 I lay down and slept; I awoke, for Yahweh protected me.
Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
6 I will not be afraid of the multitudes of people who have set themselves against me on every side.
Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
7 Rise up, Yahweh! Save me, my God! For you will hit all my enemies on the jaw; you will break the teeth of the wicked.
Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
8 Salvation comes from Yahweh. May your blessings be on your people. (Selah)
Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)