< Psalms 122 >

1 A song of ascents, of David. I was glad when they said to me, “Let us go to the house of Yahweh.”
Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
2 Jerusalem, our feet are standing within your gates!
Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
3 Jerusalem, built as a city carefully planned!
An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
4 The tribes go up to Jerusalem—the tribes of Yahweh— as a testimony for Israel, to give thanks to the name of Yahweh.
A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
5 There thrones of judgment were set, thrones of the house of David.
A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
6 Pray for the peace of Jerusalem! “May those who love you have peace.
Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
7 May there be peace within the walls that defend you, and may they have peace within your fortresses.”
Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
8 For the sake of my brothers and my friends I will say, “May there be peace within you.”
Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
9 For the sake of the house of Yahweh our God, I will seek good for you.
Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.

< Psalms 122 >