< Psalms 101 >
1 A psalm of David. I will sing of covenant faithfulness and justice; to you, Yahweh, I will sing praises.
Ta Dawuda. Zabura ce. Zan rera wa ƙauna da adalcinka; gare ka, ya Ubangiji, zan rera yabo.
2 I will walk in the way of integrity. Oh, when will you come to me? I will walk with integrity within my house.
Zan yi hankali ga yin rayuwa marar zargi, yaushe za ka zo gare ni? Zan bi da sha’anin gidana da zuciya marar abin zargi
3 I will not put wrongdoing before my eyes; I hate worthless evil; it will not cling to me.
Ba zan kafa a gaban idanuna 1 wani abu marar kyau ba. Na ƙi jinin ayyukan mutane marasa aminci; ba za su manne mini ba.
4 Perverse people will leave me; I am not loyal to evil.
Mutane masu mugun zuciya za su nesa da ni; ba abin da zai haɗa ni da mugunta.
5 I will destroy whoever secretly slanders his neighbor. I will not tolerate anyone who has a proud demeanor and an arrogant attitude.
Duk wanda ya yi ɓatanci wa maƙwabcinsa a ɓoye shi za a kashe; duk mai renin wayo da mai girman kai, ba zan jure masa ba.
6 I will look to the faithful of the land to sit at my side. Those who walk in the way of integrity may serve me.
Idanuna za su kasance a kan amintattu a cikin ƙasar, don su zauna tare da ni; tafiyarsa ba ta da zargi zai yi mini hidima.
7 Deceitful people will not remain within my house; liars will not be welcome before my eyes.
Babu mai ruɗun da zai zauna a gidana; babu mai ƙaryan da zai tsaya a gabana.
8 Morning by morning I will destroy all the wicked from the land; I will remove all evildoers from the city of Yahweh.
Kowace safiya zan rufe bakunan dukan mugaye a ƙasar; zan yanke kowane mai aikata mugunta daga birnin Ubangiji.