< Numbers 13 >

1 Then Yahweh spoke to Moses. He said,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “Send some men to examine the land of Canaan, which I have given to the people of Israel. Send a man from every tribe of their ancestors. Each man must be a leader among them.”
“Ka aiki waɗansu mutane zuwa ƙasar Kan’ana, wadda nake ba Isra’ilawa. Daga kowace kabila, ka aiki ɗaya daga cikin shugabanninta.”
3 Moses sent them from the wilderness of Paran, so that they might obey Yahweh's command. All of them were leaders among the people of Israel.
Saboda haka bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya aike su daga Hamadan Faran. Dukansu kuwa shugabanni ne na Isra’ilawa.
4 These were their names: from the tribe of Reuben, Shammua son of Zaccur;
Shugabannin kuwa su ne, Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ruben;
5 from the tribe of Simeon, Shaphat son of Hori;
Shafat ɗan Hori, daga kabilar Simeyon;
6 from the tribe of Judah, Caleb son of Jephunneh;
Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
7 from the tribe of Issachar, Igal son of Joseph;
Igal ɗan Yusuf, daga kabilar Issakar;
8 from the tribe of Ephraim, Hoshea son of Nun;
Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Efraim;
9 from the tribe of Benjamin, Palti son of Raphu;
daga kabilar Benyamin, Falti ɗan Rafu;
10 from the tribe of Zebulun, Gaddiel son of Sodi;
Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zebulun;
11 from the tribe of Joseph (that is to say, from the tribe Manasseh), Gaddi son of Susi;
Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manasse (wata kabilar Yusuf);
12 from the tribe of Dan, Ammiel son of Gemalli;
Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan;
13 from the tribe of Asher, Sethur son of Michael;
Setur ɗan Mika’ilu, daga kabilar Asher;
14 from the tribe of Naphtali, Nahbi son of Vophsi;
Nabi ɗan Bofsi, daga kabilar Naftali;
15 from the tribe of Gad, Geuel son of Maki.
Geyuwel ɗan Maki, daga kabilar Gad.
16 These were the names of the men whom Moses sent to examine the land. Moses called Hoshea son of Nun by the name of Joshua.
Waɗannan su ne sunayen mutanen da Musa ya aika su binciki ƙasar. (Sai Musa ya ba Hosheya ɗan Nun, suna Yoshuwa.)
17 Moses sent them to examine the land of Canaan. He said to them, “Approach from the Negev and go up into the hill country.
Sa’ad da Musa ya aike su domin su binciki Kan’ana ya ce, “Ku haura, ku ratsa ta Negeb har zuwa ƙasar tudu.
18 Examine the land to see what it is like. Observe the people who live there, whether they are strong or weak, and whether they are few or many.
Ku ga yadda ƙasar take, ku ga ko mutanen da suke zama a can ƙarfafa ne, ko raunannu, ko su kima ne, ko kuma suna da yawa.
19 See what the land is like where they live. Is it good or bad? What cities are there? Are they like camps, or are they fortified cities?
Wace irin ƙasa ce suke zama a ciki, Mai kyau ce, ko mummuna? Waɗanne irin birane ne suke zama a ciki? Suna da katanga, ko babu?
20 See what the land is like, whether it is good for growing crops or not, and whether there are trees there or not. Be brave and bring back samples of the land's produce.” Now the time was the season for the first ripe grapes.
Yaya ƙasar take? Tana da wadata, ko babu? Akwai itatuwa, ko babu? Ku yi iya ƙoƙarinku ku ɗebo daga cikin albarkar ƙasar ku kawo.” (Lokacin farkon nunan inabi ne.)
21 So the men went up and examined the land from the wilderness of Zin to Rehob, near Lebo Hamath.
Saboda haka suka haura, suka binciki ƙasar daga Hamadan Zin har zuwa Rehob, wajen Lebo Hamat.
22 They went up from the Negev and arrived at Hebron. Ahiman, Sheshai, and Talmai, clans descended from Anak, were there. Now Hebron had been built seven years before Zoan in Egypt.
Suka kuma haura ta Negeb, suka iso Hebron, inda Ahiman, da Sheshai, da Talmai, zuriyar Anak, suke zama. (An gina Hebron da shekara bakwai kafin a gina Zowan a Masar.)
23 When they reached the Valley of Eshkol, they cut down a branch with a cluster of grapes. They carried it on a staff between two of their group. They also brought pomegranates and figs.
Da suka iso Kwarin Eshkol, sai suka yanko reshe guda na nonon inabi tare da’ya’yansa cunkus. Mutum biyu suka ɗauka shi rataye a sanda a kafaɗarsu, suka haɗa tare da rumman da kuma ɓaure.
24 That place was named the Valley of Eshkol, because of the grape cluster that the people of Israel cut down there.
Sai aka kira wurin Kwarin Eshkol saboda nonon inabin da suka yi cunkus, wanda Isra’ilawa suka yanko a wurin.
25 After forty days, they returned from examining the land.
A ƙarshen kwana arba’in sai suka komo daga bincikensu.
26 They came back to Moses, Aaron, and all the community of the people of Israel in the wilderness of Paran, at Kadesh. They brought back word to them and to all the community, and showed them the produce from the land.
Suka dawo wurin Musa, da Haruna, da dukan jama’ar Isra’ilawa, a Kadesh, a Hamadan Faran. A can suka ba da rahoton ga dukan taron da yake wurin, suka kuma nuna musu amfanin ƙasar.
27 They told Moses, “We reached the land to which you sent us. It certainly flows with milk and honey. Here is some produce from it.
Suka ce wa Musa, “Mun je ƙasar da ka aike mu, ƙasar tana zub da madara da zuma! Ga kuma amfaninta.
28 However, the people who make their homes there are strong. The cities are fortified and very large. We also saw descendants of Anak there.
Amma fa mazaunan can ɗin ƙarfafa ne, an kuma kewaye biranen da manya-manyan katanga. Mun kuma ga zuriyar Anak a can.
29 The Amalekites live in the Negev. The Hittites, Jebusites, and Amorites have their homes in the hill country. The Canaanites live by the sea and along the Jordan River.”
Amalekawa suna zama a Negeb; Hittiyawa, Yebusiyawa da kuma Amoriyawa, suna zama ne a ƙasar tudu. Kan’aniyawa kuma suna zama kusa da teku da kuma a bakin Urdun.”
30 Then Caleb silenced the people who were before Moses and said, “Let us go up and take possession of the land, for we are certainly able to conquer it.”
Sai Kaleb ya sa mutane suka yi shiru a gaban Musa, sai ya ce, “Ya kamata mu tafi mu mallaki ƙasar, gama lalle za mu iya cinta.”
31 But the other men who had gone with him said, “We are not able to attack the people because they are stronger than we are.”
Amma sauran mutanen da suka je tare da shi, suka ce, “Ba za mu iya kara da mutanen nan ba; sun fi mu ƙarfi.”
32 So they spread around a discouraging report to the people of Israel about the land that they had examined. They said, “The land that we looked at is a land that eats up its inhabitants. All the people whom we saw there are people of great height.
Sai suka yaɗa labari marar kyau ga Isra’ilawa game da ƙasar da suka binciko. Suka ce, “Ƙasar da muka ratsa cikinta domin mu leƙi asirinta, tana cinye waɗanda suke zama a cikinta. Dukan mutanen da muka gani a wurin, ƙatti ne.
33 There we saw giants, descendants of Anak, people who came from giants. In our own sight we were like grasshoppers in comparison with them, and this is what we were in their sight, too.”
Mun ga Nefilimawa a can (zuriyar Anak sun fito ne daga Nefilim). Sai muka ga kanmu kamar fāra ne kawai, haka kuwa muke a gare su.”

< Numbers 13 >