< Nahum 3 >
1 Woe to the city full of blood! It is all full of lies and stolen property; victims are always in her.
Kaiton birni mai zub da jini, wadda take cike da ƙarairayi, cike da ganima, wadda ba a rasa masu fāɗawa cikin wahala!
2 But now there is the noise of whips and the sound of rattling wheels, prancing horses, and bounding chariots.
Ku ji karar bulala da kwaramniyar ƙafafu, da sukuwar dawakai da girgizar kekunan yaƙi!
3 There are attacking horsemen, flashing swords, glittering spears, heaps of corpses, great piles of bodies. There is no end to the bodies; their attackers stumble over them.
Mahaya dawakai sun kunno kai, takuba suna walƙiya, māsu kuma suna ƙyali; ga ɗumbun da aka kashe ga tsibin matattu, gawawwaki ba iyaka, mutane suna tuntuɓe da gawawwaki,
4 This is happening because of the lustful actions of the beautiful prostitute, the expert in witchcraft, who sells nations through her prostitution, and peoples through her acts of witchcraft.
duk saboda yawan sha’awace-sha’awacen karuwa, mai daɗin baki, uwargidan maita, wadda ta ɓad da al’ummai ta wurin karuwancinta ta kuma ɓad da mutane ta wurin maitancinta.
5 “See, I am against you—this is the declaration of Yahweh of hosts—I will raise up your skirt over your face and show your private parts to the nations, your shame to the kingdoms.
“Ina gāba da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kware fatarinki a idonki. Zan nuna wa al’ummai tsiraicinki, masarautai kuma kunyarki.
6 I will throw disgusting filth on you and make you vile; I will make you someone that everyone will look at.
Zan watsa miki ƙazanta, in yi miki wulaƙanci in kuma mai da ke abin reni.
7 It will come about that everyone who looks at you will flee from you and say, 'Nineveh is destroyed; who will weep for her?' Where can I find anyone to comfort you?”
Duk wanda ya gan ki zai gudu daga gare ki yana cewa, ‘Ninebe ta lalace, wa zai yi makoki domin ta?’ Ina zan sami wani wanda zai yi miki ta’aziyya?”
8 Nineveh, are you better than Thebes, that was built on the Nile River, that had water around her, whose defense was the ocean, whose wall was the sea itself?
Kin fi Tebes ne da take a bakin Nilu, da ruwa yake kewaye da ita? Rafi shi ne kāriyarta, ruwanta kuma katanga.
9 Cush and Egypt were her strength, and there was no end to it; Put and Libya were allies to her.
Kush da kuma Masar su ne ƙarfinta marar iyaka; Fut da Libiya suna cikin mataimakanta.
10 Yet Thebes was carried away; she went into captivity; her young children were dashed in pieces at the head of every street; her enemies threw lots for her honorable men, and all her great men were bound in chains.
Duk da haka an tafi da ita ta kuma tafi bauta. Aka fyaɗa ƙanananta da ƙasa aka yayyanka su gunduwa-gunduwa a kan kowane titi. Aka jefa ƙuri’a a kan manyan mutanenta, aka daure manyan mutanenta da sarƙoƙi.
11 You also will become drunk; you will try to hide, and you will also look for a refuge from your enemy.
Ke ma za ki bugu, za ki ɓuya. Ki kuma nemi mafaka daga wurin abokin gāba.
12 All your fortresses will be like fig trees with the earliest ripe figs: if they are shaken, they fall into the mouth of the eater.
Dukan kagarunki suna kama da itatuwan ɓaure da’ya’yansu da suka nuna. Da an girgiza, sai ɓaure su zuba a bakin mai sha.
13 See, the people among you are women; the gates of your land have been opened wide to your enemies; fire has devoured their bars.
Dubi mayaƙanki, duk mata ne! Ƙofofin ƙasarki a buɗe suke ga abokan gābanki, wuta ta cinye madogaransu.
14 Go draw water for the siege; strengthen your fortresses; go into the clay and tread the mortar; pick up the molds for the bricks.
Ki ja ruwa gama za a kewaye ki da yaƙi. Ki ƙara ƙarfin kagaranki! Ki kwaɓa laka, ki sassaƙa turmi ki gyara abin yin tubali!
15 Fire will devour you there, and the sword will destroy you. It will devour you as young locusts devour everything. Make yourselves as many as the young locusts, as many as the full-grown locusts.
A can wuta za tă cinye ki; takobi zai sare ki, kuma kamar fāra, za a cinye ki. Ki riɓaɓɓanya kamar fāra, ki riɓaɓɓanya kamar fārin ɗango!
16 You have multiplied your merchants more than the stars in the heavens; but they are like young locusts: they plunder the land and then fly away.
Kin ƙara yawan masu kasuwancinki har sai da suka fi taurarin sama. Amma kamar fāra sun cinye ƙasar sa’an nan suka tashi, suka tafi.
17 Your princes are as many as the full-grown locusts, and your generals are like swarms of them that camp in the walls on a cold day. But when the sun rises they fly away to no one knows where.
Masu tsaronki suna kama da fāri ɗango, shugabanninki sun yi cincirindo kamar fārin ɗango da suka sauka a kan bango a rana mai sanyi, amma da rana ta fito, duk za su tashi su tafi, ba kuma wanda ya san inda suka nufa.
18 King of Assyria, your shepherds are asleep; your rulers are lying down resting. Your people are scattered on the mountains, and there is no one to gather them.
Ya sarkin Assuriya, makiyayanka sun yi barci; manyan mutanenka sun kwanta su huta. An watsar da mutanenka a cikin duwatsu, ba wanda zai tattaro su.
19 No healing is possible for your wounds. Your wounds are severe. Everyone who hears the news about you will clap their hands in joy over you. Who has escaped your constant wickedness?
Ba abin da zai warkar da rauninka; rauninka ya yi muni. Duk wanda ya ji labarinka zai tafa hannuwansa saboda farin cikin fāɗuwarka, gama wane ne bai ji jiki a hannunka ba?