< Luke 7 >

1 After Jesus had finished everything he was saying in the hearing of the people, he entered Capernaum.
Bayan Yesu ya gama gaya wa mutanen dukan waɗannan abubuwa, sai ya shiga Kafarnahum.
2 Now a centurion had a slave who was highly regarded by him, and he was sick and about to die.
A can, akwai wani bawan wani jarumin yana ciwo, yana kuma a bakin mutuwa. Maigidansa kuwa yana sonsa sosai.
3 When the centurion heard about Jesus, he sent to him elders of the Jews, asking him to come and heal his servant.
Jarumin sojan ya ji labarin Yesu, sai ya aiki waɗansu dattawan Yahudawa wajensa, yana roƙonsa yă zo yă warkar da bawansa.
4 When they had come to Jesus, they asked him earnestly, saying, “He is worthy to have you do this for him,
Da suka isa wurin Yesu, sai suka roƙe shi sosai, suka ce, “Wannan mutum, ai, ya dace a yi masa haka,
5 because he loves our nation, and he is the one who built the synagogue for us.”
gama yana ƙaunar al’ummarmu ta Yahudawa, har ya gina majami’armu.”
6 So Jesus continued on his way with them. But when he was not far from the house, the centurion sent friends to say to him, “Lord, do not trouble yourself, because I am not worthy for you to come under my roof.
Sai Yesu ya tafi tare da su. Da ya yi kusa da gidan, sai jarumin nan, ya aiki abokai su ce masa, “Ubangiji, kada ka dami kanka, gama ban isa ka shiga gidana ba.
7 For this reason I did not even consider myself worthy to come to you, but just say a word and my servant will be healed.
Shi ya sa ban ma ga na isa in zo wurinka ba. Amma ka yi magana kawai, bawana zai warke.
8 For I also am a man who is under authority, with soldiers under me. I say to this one, 'Go,' and he goes, and to another one, 'Come,' and he comes, and to my servant, 'Do this,' and he does it.”
Gama ni kaina, mutum ne a ƙarƙashin iko, akwai kuma sojoji a ƙarƙashin ikona. Nakan ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai yă tafi, ga wani kuma in ce, ‘Zo nan,’ sai yă zo. Nakan kuma ce wa bawana, ‘Yi abu kaza,’ sai yă yi.”
9 When Jesus heard this, he was amazed at him, and turning to the crowd following him said, “I say to you, not even in Israel have I found such faith.”
Da Yesu ya ji haka, sai ya yi mamaki sosai. Ya juya ya wa taron da yake bin sa, “Ina faɗa muku, ban taɓa samun irin bangaskiya mai girma haka ko cikin Isra’ila ba.”
10 When those who had been sent returned to the house, they found the servant was well.
Sai mutanen da aka aika, suka koma gida, suka tarar bawan ya warke.
11 Soon after that, Jesus went to a town called Nain, and his disciples and a great crowd went with him.
Ba a daɗe ba, sai Yesu ya tafi wani garin da ake kira Nayin. Almajiransa da taro mai yawa suka tafi tare da shi.
12 As he came near to the gate of the town, behold, a man who had died was being carried out, the only son of his mother (who was a widow), and a rather large crowd from the town was with her.
Da ya yi kusa da ƙofar garin, sai ga wata gawa ana fitowa da ita. Shi ne ɗa kaɗai ga mahaifiyarsa, ita kuma gwauruwa ce. Taro mai yawa daga garin yana tare da ita.
13 When the Lord saw her, he was deeply moved with compassion for her and said to her, “Do not cry.”
Da Ubangiji ya gan ta, sai ya ji tausayinta ya ce, “Kada ki yi kuka.”
14 Then he went up and touched the wooden frame on which they carried the body, and those carrying it stood still. He said, “Young man, I say to you, arise.”
Yesu ya je ya taɓa akwatin gawar, sai masu ɗaukarsa suka tsaya cik. Sai ya ce, “Saurayi, na ce maka, tashi!”
15 The dead man sat up and began to speak, and Jesus gave him to his mother.
Sai mamacin ya tashi zaune, ya fara magana. Yesu kuma ya ba da shi ga mahaifiyarsa.
16 Then fear overcame all of them, and they kept praising God, saying, “A great prophet has been raised among us” and “God has looked upon his people.”
Sai tsoro ya kama su duka, suka yabi Allah, suna cewa, “Babban annabi ya bayyana a cikinmu. Allah ya zo domin yă taimaki mutanensa.”
17 This news about Jesus spread throughout the whole of Judea and all the neighboring regions.
Wannan labarin game da Yesu, ya bazu ko’ina a Yahudiya da kewayenta.
18 John's disciples told him about all these things.
Almajiran Yohanna suka gaya masa dukan waɗannan abubuwa. Sai ya kira biyu daga cikinsu,
19 Then John called two of his disciples and sent them to the Lord to say, “Are you the one who is to come, or should we look for another?”
ya aike su wurin Ubangiji, su tambaya su ce, “Kai ne wanda zai zo, ko kuma mu saurari wani dabam?”
20 When they had come near to Jesus, the men said, “John the Baptist has sent us to you to say, 'Are you the one who is coming, or should we look for another?'”
Da mutanen suka iso wurin Yesu, sai suka ce, “Yohanna Mai Baftisma ne ya aike mu wurinka, mu yi tambaya, ‘Ko kai ne wanda zai zo, ko kuma mu saurari wani dabam?’”
21 In that hour he healed many people from sicknesses and afflictions and from evil spirits, and to many blind people he gave sight.
A daidai lokacin nan, Yesu ya warkar da mutane da yawa masu ciwo, masu cututtuka, da kuma masu mugayen ruhohi. Ya kuma ba makafi da yawa ganin gari.
22 Jesus answered and said to them, “After you have gone on your way, report to John what you have seen and heard. Blind people are receiving sight, lame people are walking, lepers are being cleansed, deaf people are hearing, people who have died are being raised back to life, and needy people are being told the good news.
Sai ya amsa wa almajiran Yohanna ya ce, “Ku koma ku faɗa wa Yohanna abin da kuka ji, da abin da kuka gani. Makafi suna ganin gari, guragu suna tafiya, ana warkar da waɗanda suke da kuturta, kurame suna ji, ana tā da matattu, ana kuma yi wa matalauta wa’azin bishara.
23 The person who does not stop believing in me because of my actions is blessed.”
Mai albarka ne mutumin da bai yi shakkar bangaskiyar da yake da ita a kaina ba.”
24 After John's messengers had gone away, Jesus began to say to the crowds about John, “What did you go out into the desert to see? A reed shaken by the wind?
Bayan almajiran Yohanna suka tafi, sai Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yohanna ya ce, “Me kuka je kallo a hamada? Ciyawar da iska take kaɗawa ne?
25 But what did you go out to see? A man dressed in soft clothes? Look, those who wear expensive clothing and who live in luxury are in kings' palaces.
In ba haka ba, to, me kuka je kallo? Mutum mai sanye da tufafi masu kyau ne? A’a, masu sa kayan tsada da suke cikin annashuwa, ai, a fada suke.
26 But what did you go out to see? A prophet? Yes, I say to you, and more than a prophet.
Amma me kuka je kallo? Annabi? I, ina kuma faɗa muku, ya ma fi annabi.
27 This is he of whom it is written, 'See, I am sending my messenger before your face, who will prepare your way before you.'
Wannan shi ne wanda aka rubuta game da shi cewa, “‘Zan aiko da ɗan saƙona yă sha gabanka, wanda zai shirya hanya, a gabanka.’
28 I say to you, among those born of women none is greater than John. Yet the one who is least in the kingdom of God is greater than he is.”
Ina faɗa muku, a cikin duk waɗanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yohanna girma. Duk da haka wanda ya fi ƙasƙanta a Mulkin Allah ya fi shi.”
29 (When all the people heard this, including the tax collectors, they declared that God is righteous, because they had been baptized with the baptism of John.
(Dukan mutane, har da masu karɓar haraji, da suka ji kalmomin Yesu, sai suka yarda cewa hanyar Allah gaskiya ce, domin Yohanna ne ya yi musu baftisma.
30 But the Pharisees and the experts in Jewish law rejected God's purpose for themselves, because they had not been baptized by John.)
Amma Farisiyawa da masanan dokoki, suka ƙi nufin Allah game da su, domin Yohanna bai yi musu baftisma ba.)
31 “To what, then, can I compare the people of this generation? What are they like?
Yesu ya ci gaba da cewa, “To, da me zan kwatanta mutanen zamanin nan? Kamar me suke?
32 They are like children playing in the marketplace, who sit and call to one another and say, 'We played a flute for you, and you did not dance. We sang a funeral song, and you did not cry.'
Suna kama da yaran da suke zama a bakin kasuwa, suna kiran juna, suna cewa, “‘Mun busa muku sarewa, amma ba ku yi rawa ba, Mun kuma yi muku waƙar makoki, ba ku kuma yi kuka ba.’
33 For John the Baptist came eating no bread and drinking no wine, and you say, 'He has a demon.'
Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo, ba ya cin burodi, ba ya shan ruwan inabi, sai kuka ce, ‘Ai, yana da aljani.’
34 The Son of Man came eating and drinking, and you say, 'Look, he is a gluttonous man and a drunkard, a friend of tax collectors and sinners!'
Ɗan Mutum ya zo yana ci, yana sha, sai kuka ce, ‘Ga mai yawan ci, mashayi, da kuma abokin masu karɓar haraji da masu zunubi.’
35 But wisdom is justified by all her children.”
Amma akan tabbatar da hikima ta gaskiya bisa ga dukan’ya’yanta.”
36 Now one of the Pharisees invited Jesus to eat with him. So after Jesus entered into the Pharisee's house, he reclined at the table to eat.
To, ana nan, sai ɗaya daga cikin Farisiyawa ya gayyaci Yesu cin abincin yamma a gidansa, ya kuwa tafi gidan Bafarisiyen, ya zauna a tebur.
37 Behold, there was a woman in the city who was a sinner. When she found out that he was reclining at the table in the Pharisee's house, she brought an alabaster jar of perfumed oil.
Da wata mace wadda ta yi rayuwar zunubi a wannan gari ta ji Yesu yana cin abinci a gidan Bafarisiyen, sai ta kawo ɗan tulun turaren alabasta,
38 As she stood behind him near his feet, weeping, she began to wet his feet with her tears, and she wiped them with the hair of her head and kissed his feet and anointed them with perfumed oil.
ta kuma tsaya daga bayansa, wajen ƙafafunsa tana kuka, sai hawayenta sun fara zuba a ƙafafunsa. Sai ta goge su da gashin kanta, ta sumbace su, sa’an nan ta shafa musu turare.
39 When the Pharisee who had invited Jesus saw this, he thought to himself, saying, “If this man were a prophet, then he would know who and what type of woman is touching him, that she is a sinner.”
Da Bafarisiyen da ya gayyace shi, ya ga wannan, sai ya ce a ransa, “Da mutumin nan annabi ne, da ya san ko wace ce take taɓansa, da kuma irin macen da take, cewa mai zunubi ce.”
40 Jesus responded and said to him, “Simon, I have something to say to you.” He said, “Say it, Teacher!”
Sai Yesu ya ce masa, “Siman, ina da abin da zan faɗa maka.” Shi kuwa ya ce, “Malam sai ka faɗa.”
41 Jesus said, “A certain moneylender had two debtors. The one owed five hundred denarii, and the other fifty.
Yesu ya ce, “An yi waɗansu mutum biyu da suke riƙe bashin mai ba da rance. Ana bin guda dinari ɗari biyar, ɗayan kuma hamsin.
42 When they could not pay him, he forgave them both. Therefore, which of them will love him more?”
Dukan biyun suka gagara biyansa, sai ya yafe musu. To, a ganinka, wa zai fi ƙaunar mutumin nan?”
43 Simon answered him and said, “I suppose the one whom he forgave the most.” Jesus said to him, “You have judged correctly.”
Siman ya amsa ya ce, “A ganina, wanda aka yafe wa mai yawa ne.” Sai Yesu ya ce, “Ka faɗa daidai.”
44 Jesus turned to the woman and said to Simon, “You see this woman. I have entered into your house. You gave me no water for my feet, but she has wet my feet with her tears and wiped them with her hair.
Sai ya juya wajen macen, ya ce wa Siman, “Ka ga macen nan? Na shigo gidanka, ba ka ba ni ruwa don ƙafafuna ba, amma ta wanke ƙafafuna da hawayenta, ta kuma goge su da gashin kanta.
45 You did not give me a kiss, but from the time I came in she did not stop kissing my feet.
Ba ka yi mini sumba ba, amma tun shigowata a nan, macen nan ba tă daina sumbar ƙafafuna ba.
46 You did not anoint my head with oil, but she has anointed my feet with perfumed oil.
Ba ka shafa mai a kaina ba, amma ta zubo turare a ƙafafuna.
47 Therefore I say to you, her sins, which were many, have been forgiven—for she loved much. But the one who is forgiven little, loves little.”
“Saboda haka ina gaya maka, zunubanta masu yawa, an gafarta mata, gama ƙaunarta mai yawa ce. Amma wanda aka gafarta wa kaɗan kuwa, yakan nuna ƙauna kaɗan.”
48 Then he said to her, “Your sins are forgiven.”
Sai Yesu ya ce mata, “An gafarta miki zunubanki.”
49 Those reclining together began to say among themselves, “Who is this that even forgives sins?”
Sauran baƙin suka fara ce wa juna, “Wane ne wannan, wanda har yake gafarta zunubai?”
50 Then Jesus said to the woman, “Your faith has saved you. Go in peace.”
Yesu ya ce wa macen, “Bangaskiyarki ta cece ki, ki sauka lafiya.”

< Luke 7 >