< Lamentations 2 >

1 The Lord has covered the daughter of Zion under the cloud of his anger. He has thrown the splendor of Israel down from heaven to earth. He has not remembered his footstool on the day of his anger.
Yadda Ubangiji ya rufe Diyar Sihiyona da gizagizan fushi! Ya jefar da darajar Isra’ila daga sama zuwa ƙasa; bai tuna da wurin ɗora ƙafafunsa ba a ranar fushinsa.
2 The Lord has swallowed up and has had no compassion on all the towns of Jacob. In the days of his anger he has thrown down the fortified cities of the daughter of Judah; in dishonor he has brought down to the ground the kingdom and its rulers.
Ubangiji ya hallakar da wurin zaman Yaƙub ba tausayi; A cikin fushinsa kuma zai rurrushe kagaran Diyar Yahuda. Ya ƙasƙantar da mulki da masu mulki.
3 With fierce anger he has cut off every horn of Israel. He has withdrawn his right hand from before the enemy. He has burned up Jacob like a blazing fire that devours everything around it.
A cikin zafin fushi ya fasa kowane ƙaho na Isra’ila. Ya janye hannun damansa sa’ad da maƙiyi ya zo. Ya yi ƙuna a cikin Yaƙub kamar wuta mai ƙone duk abin da yake kusa da ita.
4 Like an enemy he has bent his bow toward us, with his right is ready to shoot. He has slaughtered all who had been so pleasing to him in the tent of the daughter of Zion; he has poured out his wrath like fire.
Kamar abokin gāba, ya ɗana bakansa; hannun damansa na shirye. Kamar maƙiyi, ya kashe duk wanda idonsa ya ji daɗin gani; ya zuba fushinsa kamar wuta a kan tenti na Diyar Sihiyona.
5 The Lord has become like an enemy. He has swallowed up Israel. He has swallowed up all her palaces. He has destroyed her strongholds. He has increased mourning and lamentation within the daughter of Judah.
Ubangiji kamar maƙiyi ne; ya hallaka Isra’ila. Ya hallaka wurarenta duka ya kuma hallaka kagaranta. Ya ƙara yawan makoki da baƙin ciki wa Diyar Yahuda.
6 He has attacked his tabernacle like a garden hut. He has destroyed the place of the solemn assembly. Yahweh has caused both solemn assembly and Sabbath to be forgotten in Zion, for he has despised both king and priest in the indignation of his anger.
Ya rushe haikalinsa kamar lambu; ya hallaka wurin yi masa sujada. Ubangiji ya sa Sihiyona ta manta da bukukkuwanta da kuma ranakunta na Asabbaci; a cikin zafin fushinsa ya watsar da sarki da firist.
7 The Lord has rejected his altar and disowned his sanctuary. He has given over the walls of her palaces into the hand of the enemy. They have raised a shout in the house of Yahweh, as on the day of an appointed feast.
Ubangiji ya ƙi bagadensa ya kuma yi wofi da haikalinsa. Ya ba maƙiyinta fadodinta; suka yi sowa a cikin gidan Ubangiji kamar a ranar da ake yin biki.
8 Yahweh decided to destroy the city wall of the daughter of Zion. He has stretched out the measuring line and has not withheld his hand from destroying the wall. He has made the ramparts and wall to lament; together they wasted away.
Ubangiji ya ƙuduri niyya yă rushe bangon da yake kewaye da Diyar Sihiyona. Ya auna da igiyar awo bai fasa hallaka ta ba. Ya sa katanga da katanga duk suka lalace.
9 Her gates have sunk into the ground; he has destroyed and broken the bars of her gate. Her king and her princes are among the nations, the law is no more and her prophets find no vision from Yahweh.
Ƙofofinta sun nutse a cikin ƙasa; ya kakkarya ƙarafanta. Sarakunanta da’ya’yan sarakunanta duk an kai su bauta cikin waɗansu ƙasashe, babu sauran doka, annabawa kuma ba su samun wahayi daga wurin Ubangiji.
10 The elders of the daughter of Zion sit on the ground in silence. They have thrown dust on their heads and put on sackcloth. The virgins of Jerusalem have bowed their heads to the ground.
Dattawan Diyar Sihiyona sun zauna shiru a ƙasa; suka kuma sa rigar buhu.’Yan matan Urushalima suka sunkuyar da kawunansu ƙasa.
11 My eyes have failed from their tears; my stomach churns; my inner parts are poured out to the ground because of the destruction of the daughter of my people, children and infants faint in the streets of the city.
Idanuna sun dushe don yawan kuka, raina na cike da baƙin ciki; zuciyata ta karaya domin mutanena sun hallaka, domin yara da jarirai suna suma a kan hanyoyi a cikin birni.
12 They say to their mothers, “Where is grain and wine?” as they faint like a wounded man in the streets of the city, their lives are poured out on the bosom of their mothers.
Suna ce wa uwayensu, “Ina burodi da ruwan inabi?” Yayinda suke suma kamar mutanen da aka ji masu ciwo a cikin birni, sa’ad da suke mutuwa a hannuwan uwayensu.
13 What can I say to you, daughter of Jerusalem? To what can I compare to you, that I may comfort you, virgin daughter of Zion? Your wound is as great as the sea. Who can heal you?
Me zan ce miki? Da me zan kwatanta ki, ke Diyar Urushalima? Da me zan misalta ki, yadda zan iya yi miki ta’aziyya, Ke Budurwa Diyar Sihiyona? Ciwonki yana da zurfi kamar teku. Wane ne zai iya warkar da ke?
14 Your prophets have seen false and worthless visions for you. They have not exposed your iniquity to restore your fortunes, but for you they gave utterances that are false and misleading.
Wahayin annabawanki ƙarya ne kuma marasa amfani; ba su tona zunubanki ba yadda za su iya ceto ki daga bauta ba. Sun yi miki annabcin ƙarya marar amfani.
15 All those who pass along the road clap their hands at you. They hiss and shake their heads against the daughter of Jerusalem and say, “Is this the city that they called 'The Perfection of Beauty,' 'The Joy for All of Earth'?”
Duk masu wucewa suna yi miki tafi na reni; suna yi wa Diyar Urushalima tsaki suna kaɗa kai suna cewa, “Wannan ne birnin da aka ce kyakkyawa ne, mai farantawa dukan duniya rai?”
16 All your enemies open their mouths against you. They sneer and grind their teeth in rage and say, “We have swallowed her up! This is the day we have waited for! We have lived to see it!”
Maƙiyanki duka suna ta surutu game da ke; suna tsaki suna cizon haƙora suna cewa, “Mun hallaka ta. Wannan ce ranar da muke jira; yau mun gan ta.”
17 Yahweh has done what he planned to do. He has fulfilled his word. He has overthrown you without pity, for he has permitted the enemy to rejoice over you; he has lifted up the horn of your enemies.
Ubangiji ya yi abin da ya shirya; ya cika maganarsa, wadda ya umarta tun daɗewa. Ya jefar da ke ba tausayi, ya bari maƙiya sun yi nasara da ke, ya ɗaukaka ƙahon maƙiyanki.
18 Their heart cried out to the Lord, walls of the daughter of Zion! Make your tears flow down like a river day and night. Give yourself no relief, your eyes no relief.
Zuciyar mutane ta yi kuka ga Ubangiji. Ya bangon Diyar Urushalima, bar hawayenki su zuba kamar rafi dare da rana; kada ki huta, kada idanunki su huta.
19 Arise, cry out in the night, at the beginning of the night watches! Pour out your heart like water before the face of the Lord. Lift up your hands to him for the lives of your children who faint with hunger at the corner of every street.”
Ki tashi, ki yi kuka cikin dare, dare na yi sai ki fara kuka; kina buɗewa Ubangiji zuciyarki. Ki ɗaga hannuwanki gare shi domin rayukan’ya’yanki, waɗanda suka suma don yunwa a kan kowane titi.
20 See, Yahweh, and consider those you have dealt in this way. Should women eat the fruit of their wombs, the children whom they have cared for? Should priest and prophet be slaughtered in the sanctuary of the Lord?
“Ka duba, ka gani ya Ubangiji. Wane ne ka taɓa yi wa haka? Ko ya kamata uwaye su ci’ya’yansu,’ya’yan da suka yi reno? Ko ya kamata a kashe firistoci da annabawa a cikin haikalin Ubangiji?
21 Both the young and the old lie on the dust of the streets. My young women and my young men have fallen by the sword; you have slaughtered them without taking pity on them.
“Matasa da tsofaffi duk suna kwanciya a cikin ƙurar tituna; an karkashe matasa da’yan matana da takobi. Ka kashe su a ranar fushinka; ka kashe su ba tausayi.
22 You have summoned, as you would call the people to a feast day, my terrors on every side, on the day of the anger of Yahweh no one escaped or survived; those I cared for and raised, my enemy has destroyed.
“Kamar yadda kake yin gayyata a ranar biki, haka kake kawo mini tsoro a kowane gefe. A ranar fushin Ubangiji ba mai tserewa ba wanda zai tsira; maƙiyina ya kashe waɗanda na yi renonsu, na kuma lura da su.”

< Lamentations 2 >