< Judges 10 >

1 After Abimelech, Tola son of Puah son of Dodo, a man from Issachar who lived in Shamir, in the hill country of Ephraim, arose to deliver Israel.
Bayan zamanin Abimelek, sai Tola ɗan Fuwa ɗan Dodo daga Issakar ya tashi don yă ceci Isra’ila. Yana zama a Shamir a ƙasar tudu ta Efraim.
2 He judged Israel twenty-three years. He died and was buried in Shamir.
Ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin da uku sa’an nan ya mutu, aka kuma binne shi a Shamir.
3 He was followed by Jair the Gileadite. He judged Israel twenty-two years.
Bayansa kuma sai Yayir daga Gileyad, wanda ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin da biyu.
4 He had thirty sons who rode on thirty donkeys, and they had thirty cities, which are called Havvoth Jair to this day, which are in the land of Gilead.
Yana’ya’ya talatin, waɗanda suke hawan jakuna talatin. Sun shugabanci birane talatin a Gileyad, har wa yau ana ce da biranen Hawwot Yayir.
5 Jair died and was buried in Kamon.
Sa’ad da Yayir ya mutu, sai aka binne shi a Kamon.
6 The people of Israel added to the evil they had done in the sight of Yahweh and worshiped the Baals, the Ashtoreths, the gods of Aram, the gods of Sidon, the gods of Moab, the gods of the people of Ammon, and the gods of the Philistines. They abandoned Yahweh and no longer worshiped him.
Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji. Suka shiga bautar Ba’al da Ashtarot, da kuma allolin Aram, allolin Sidon, allolin Mowab, Ammonawa da kuma allolin Filistiyawa. Kuma domin Isra’ilawa sun bar Ubangiji ba su ƙara bauta masa ba,
7 Yahweh burned with anger toward Israel, and he sold them into the hand of the Philistines and into the hand of the Ammonites.
sai ya fusata da su. Ya sayar da su ga hannun Filistiyawa da Ammonawa,
8 They crushed and oppressed the people of Israel that year, and for eighteen years they oppressed all the people of Israel who were beyond the Jordan in the land of the Amorites, which is in Gilead.
waɗanda suka fatattake su a shekarar suka kuma ragargaza su. Shekara goma sha takwas suka yi ta danne dukan Isra’ilawan da suke gabashin Urdun a Gileyad, ƙasar Amoriyawa.
9 Then the Ammonites crossed over the Jordan to fight against Judah, against Benjamin, and against the house of Ephraim, so that Israel was greatly distressed.
Ammonawa su ma suka haye Urdun domin su yi yaƙi da Yahuda, Benyamin da kuma gidan Efraim; Isra’ila kuwa suka kasance cikin wahala ƙwarai da gaske.
10 Then the people of Israel called out to Yahweh, saying, “We have sinned against you, because we abandoned our God and worshiped the Baals.”
Sa’an nan Isra’ilawa suka yi kuka ga Ubangiji, suka ce, “Mun yi maka zunubi, mun bar Allahnmu muka shiga bautar Ba’al.”
11 Yahweh said to the people of Israel, “Did I not deliver you from the Egyptians, the Amorites, the Ammonites, the Philistines,
Ubangiji ya ce, “Sa’ad da Masarawa, Amoriyawa, Ammonawa, Filistiyawa,
12 and also from the Sidonians? The Amalekites and the Maonites oppressed you; you called out to me, and I delivered you from their power.
Sidoniyawa, Amalekawa da kuma mutanen Mawon suka wulaƙanta ku kuka kuwa yi mini kuka, ban cece ku daga hannunsu ba?
13 Yet you abandoned me again and worshiped other gods. Therefore, I will not keep adding to the times I deliver you.
Amma kuka bar ni kuka bauta wa waɗansu alloli, saboda haka ni ma ba zan ƙara cece ku ba.
14 Go and call out to the gods that you have worshiped. Let them rescue you when you have trouble.”
Ku tafi ku yi wa allolin da kuka zaɓa. Bari su cece ku sa’ad da kuke cikin wahala!”
15 The people of Israel said to Yahweh, “We have sinned. Do to us whatever seems good to you. Only please, rescue us this day.”
Amma Isra’ilawa suka ce wa Ubangiji, “Mu dai mun yi zunubi. Ka yi da mu abin da ka ga dama, amma muna roƙonka ka cece mu a yanzu.”
16 They got rid of the foreign gods among them and they worshiped Yahweh. Then Yahweh could bear Israel's misery no longer.
Sa’an nan suka zubar da allolin nan daga cikinsu suka bauta wa Ubangiji. Ubangiji kuwa bai ƙara daure da azabar da Isra’ila suke sha ba.
17 Then Ammonites gathered together and set up camp in Gilead. The Israelites came together and set up their camp at Mizpah.
Sa’ad da aka kira Ammonawa su yi ɗamarar yaƙi, sai su kuma kafa sansani a Gileyad, Isra’ilawa kuwa suka tattaru suka kafa sansani Mizfa.
18 The leaders of the people of Gilead said one to another, “Who is the man who will begin to fight the Ammonites? He will become the leader over all those who are living in Gilead.”
Shugabannin mutanen Gileyad suka cewa juna, “Duk wanda zai fara fāɗa wa Ammonawa shi zai zama shugaban duk waɗanda suke zama a Gileyad.”

< Judges 10 >