< Joshua 15 >

1 The assignment of land for the tribe of the people of Judah, clan by clan, extended south to the border of Edom, with the wilderness of Zin being the farthest point to the south.
An raba wa kabilar Yahuda gādonsu ta wurin yin ƙuri’a, bisa ga iyalansu, rabon ya kai har zuwa sashen Edom, zuwa Jejin Zin can kurewar kudu.
2 Their border on the south ran from the end of the Salt Sea, from the bay that faces to the south.
Iyakarsu a kudanci ta tashi tun daga kurewar kudu na Tekun Gishiri,
3 Their boundary next went out to the south of the hill of Akrabbim and passed along to Zin, and went up south of Kadesh Barnea, along by Hezron, and up to Addar, where it turned about to Karka.
zuwa kudancin Hanyar Kunama, ta ci gaba har zuwa Zin, zuwa kudancin Kadesh Barneya. Sa’an nan ta kurɗa zuwa Hezron har zuwa Addar, ta kuma karkata zuwa Karka.
4 It passed along to Azmon, went by the brook of Egypt, and came to its end at the sea. This was their south boundary.
Sai ta wuce zuwa Azmon ta haɗu da Rafin Masar, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne iyakarsu ta kudu.
5 The eastern boundary was the Salt Sea, at the mouth of the Jordan. The border on the north ran from the bay of the sea at the mouth of the Jordan.
Iyakarsu ta gabas kuwa ita ce Tekun Gishiri wadda ta zarce har zuwa gaɓar Urdun. Iyakarsu ta arewa ta fara ne daga Tekun Gishiri a bakin Urdun,
6 It went up to Beth Hoglah and passed along north of Beth Arabah. Then it went up to the Stone of Bohan the son of Reuben.
wajen Bet-Hogla ta wuce har zuwa arewancin Bet-Araba, zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.
7 Then the border went up to Debir from the Valley of Achor, and so northward, turning toward Gilgal, which is opposite the hill of Adummim, which is on the south side of the valley. Then the border passed along to the springs of En Shemesh and went to En Rogel.
Sai iyakar ta haura zuwa Debir daga Kwarin Akor ta juya arewa da Gilgal, wadda take fuskantar hawan Adummim a kudancin kwari, ta ci gaba zuwa ruwan En Shemesh, ta ɓullo ta En Rogel.
8 Then the border went up the Valley of Ben Hinnom to the south side of the Jebusite city (that is, Jerusalem). Then it went up to the top of the hill that lies over the Valley of Hinnom, on the west, which is at the northern end of the Valley of Rephaim.
Sai kuma ta gangara zuwa Kwarin Ben Hinnom a gangaren kudancin birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima). Daga can ta haura zuwa kan tudun a yammancin Kwarin Hinnom, a arewancin ƙarshen Kwarin Refayim.
9 Then the border extended from the top of the hills to the spring of Nephtoah, and went out from there to the cities of Mount Ephron. Then the border bends around to Baalah (the same as Kiriath Jearim).
Daga kan tudun, iyakar ta nufi maɓulɓular ruwa na Neftowa, ta ɓullo a garuruwan da suke a Dutsen Efron, ta gangara zuwa Ba’ala (wato, Kiriyat Yeyarim).
10 Then the border circled around west of Baalah to Mount Seir, and passed along to the side of Mount Jearim on the north (the same as Kesalon), went down to Beth Shemesh, and crossed over to Timnah.
Sa’an nan ta karkata yamma daga Ba’ala zuwa Dutsen Seyir, ta wuce ta gangaren Dutsen Yeyarim (wato, Kesalon), ta ci gaba zuwa Bet-Shemesh, ta bi zuwa Timna.
11 The border went out beside the northern hill of Ekron, and then it bends around to Shikkeron and passed along to Mount Baalah, from there it went to Jabneel. The border ended at the sea.
Ta wuce zuwa gangaren arewancin Ekron, ta juya zuwa Shikkeron, ta wuce zuwa Dutsen Ba’ala, ta kai Yabneyel, iyakarta ta ƙare a teku.
12 The western boundary was the Great Sea and its coastline. This is the border around the tribe of Judah, clan by clan.
Bakin Bahar Rum nan ne iyakar yammanci. Wannan ita ce iyakar da ta kewaye jama’ar Yahuda bisa ga iyalansu.
13 In keeping with the commandment of Yahweh to Joshua, Joshua gave Caleb son of Jephunneh an assignment of land among the tribe of Judah, Kiriath Arba, that is, Hebron (Arba was the father of Anak).
Yoshuwa ya ba Kaleb ɗan Yefunne wuri a Yahuda, Kiriyat Arba, wato, Hebron, bisa ga umarnin Ubangiji. (Arba shi ne mahaifin Anak.)
14 Caleb drove out from there the three sons of Anak: Sheshai, Ahiman and Talmai, descendants of Anak.
Daga can sai Kaleb ya kori’ya’yan Anak, maza su uku daga Hebron, wato, Sheshai, Ahiman da Talmai.
15 He went up from there against the inhabitants of Debir (Debir used to be called Kiriath Sepher).
Daga can ya nufi Debir ya yi yaƙi da mutanen da suke zama a can (Dā sunan Debir, Kiriyat Sefer ne).
16 Caleb said, “The man who attacks Kiriath Sepher and captures it, to him I will give Aksah my daughter as a wife.”
Kaleb ya ce, “Zan ba da’yata Aksa aure ga wanda zai ci Kiriyat Sefer da yaƙi.”
17 When Othniel son of Kenaz, Caleb's brother, captured it, Caleb gave him Aksah his daughter as a wife.
Otniyel ɗan Kenaz, ɗan’uwan Kaleb, ya ci Kiriyat Sefer da yaƙi; saboda haka Kaleb ya ba wa Aksa’yarsa, ya kuwa aure ta.
18 Soon after that, Aksah came to Othniel and she urged him to ask her father for a field. When she got off her donkey, Caleb said to her, “What do you want?”
Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ya zuga ta ta roƙi mahaifinta fili. Da ta sauka daga kan jakinta sai Kaleb ya tambaye ta ya ce, “Me kike so in yi miki?”
19 Aksah replied, “Do me a special favor, since you have given me the land of the Negev: Also give me some springs of water.” Then Caleb gave her the upper springs and lower springs.
Ta amsa ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman, tun da ka ba ni wuri a Negeb, ina roƙonka, ka ba ni maɓulɓulan ruwa.” Kaleb kuwa ya ba ta maɓulɓulan ruwa na tuddai da na kwari.
20 This was the inheritance of the tribe of Judah, clan by clan.
Wannan shi ne gādon kabilar Yahuda bisa ga iyalansu.
21 The cities belonging to the tribe of Judah in the extreme south, toward the border of Edom, were Kabzeel, Eder, Jagur,
Garuruwan kabilar Yahuda da suke kudu cikin Negeb zuwa iyakar Edom su ne. Kabzeyel, Eder, Yagur,
22 Kinah, Dimonah, Adadah,
Kina, Dimona, Adada,
23 Kedesh, Hazor, Ithnan,
Kedesh, Hazor, Itnan,
24 Ziph, Telem, Bealoth.
Zif, Telem, Beyalot,
25 Hazor Hadattah, Kerioth Hezron (this was also known as Hazor),
Hazor-Hadatta, Keriyot Hezron (wato, Hazor),
26 Amam, Shema, Moladah,
Amam, Shema, Molada,
27 Hazar Gaddah, Heshmon, Beth Pelet,
Hazar Gadda, Heshmon, Bet-Felet,
28 Hazar Shual, Beersheba, Biziothiah.
Hazar Shuwal, Beyersheba, Biziyotiya,
29 Baalah, Iyim, Ezem,
Ba’ala, Iyim, Ezem,
30 Eltolad, Kesil, Hormah,
Eltolad, Kesil, Horma,
31 Ziklag, Madmannah, Sansannah,
Ziklag, Madmanna, Sansanna,
32 Lebaoth, Shilhim, Ain, and Rimmon. These were twenty-nine cities in all, including their villages.
Lebayot, Shilhim, Ayin, Rimmon, jimillarsu, garuruwa da ƙauyukansu duka ashirin da tara ne.
33 In the lower hill country to the west, there were Eshtaol, Zorah, Ashnah,
Biranen da suke a filayen kwari su ne, Eshtawol, Zora; Ashna,
34 Zanoah, En Gannim, Tappuah, Enam,
Zanowa, En Gannim, Taffuwa, Enam,
35 Jarmuth, Adullam, Sokoh, Azekah,
Yarmut, Adullam, Soko, Azeka,
36 Shaaraim, Adithaim, and Gederah (that is, Gederothaim). These were fourteen cities in number, including their villages.
Sha’arayim, Aditayim, Gedera (Gederotayim ke nan). Garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu.
37 Zenan, Hadashah, Migdalgad,
Zenan, Hadasha, Migdal Gad,
38 Dilean, Mizpah, Joktheel,
Dileyan, Mizfa, Yokteyel,
39 Lachish, Bozkath, Eglon.
Lakish, Bozkat, Eglon,
40 Kabbon, Lahmas, Kitlish,
Kabbon, Lahman, Kitlish,
41 Gederoth, Beth Dagon, Naamah, Makkedah. These were sixteen cities in number, including their villages.
Gederot, Bet-Dagon, Na’ama, Makkeda, garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
42 Libnah, Ether, Ashan,
Libna, Eter, Ashan,
43 Iphtah, Ashnah, Nezib,
Yefta, Ashna, Nezib,
44 Keilah, Akzib, Mareshah. These were nine cities, including their villages.
Keyila, Akzib, Maresha, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
45 Ekron, with its surrounding towns and villages;
Ekron da ƙauyukan da suke kewaye da ita;
46 from Ekron to the Great Sea, all the settlements that were near Ashdod, including their villages.
yammancin Ekron da dukan garuruwa da ƙauyukan da suke kusa da Ashdod.
47 Ashdod, its surrounding towns, including their villages; Gaza, its surrounding towns including their villages; to the brook of Egypt, and to the Great Sea with its coastline.
Ashdod da garuruwa da kuma ƙauyukan da suke kewaye da ita, Gaza da garuruwanta da ƙauyukanta har zuwa Rafin Masar da kuma Bahar Rum.
48 In the hill country, Shamir, Jattir, Sokoh,
Birane na cikin ƙasar tuddai kuwa, su ne, Shamir, Yattir, Soko,
49 Dannah, Kiriath Sannah (that is, Debir),
Danna, Kiriyat Sanna (wato, Debir),
50 Anab, Eshtemoh, Anim,
Anab, Eshtemo, Anim,
51 Goshen, Holon, and Giloh. These were eleven cities, including their villages.
Goshen, Holon, Gilo, garuruwa goma sha ɗaya ke nan da ƙauyukansu.
52 Arab, Dumah, Eshan,
Arab, Duma, Eshan,
53 Janim, Beth Tappuah, Aphekah,
Yanum, Bet-Taffuwa, Afeka,
54 Humtah, Kiriath Arba (that is, Hebron), and Zior. These were nine cities, including their villages.
Humta, Kiriyat Arba (wato, Hebron) da Ziyor, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
55 Maon, Carmel, Ziph, Juttah,
Mawon, Karmel, Zif, Yutta
56 Jezreel, Jokdeam, Zanoah,
Yezireyel, Yokdeyam, Zanowa,
57 Kain, Gibeah, and Timnah. These were ten cities, including their villages.
Kayin, Gibeya, Timna, garuruwa goma ke nan da ƙauyukansu.
58 Halhul, Beth Zur, Gedor,
Halhul, Bet-Zur, Gedor,
59 Maarath, Beth Anoth, and Eltekon. These were six cities, including their villages.
Ma’arat, Bet-Anot, Eltekon, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
60 Kiriath Baal (that is, Kiriath Jearim), and Rabbah. These were two cities, including their villages.
Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim) da Rabba, garuruwa biyu ke nan da ƙauyukansu.
61 In the wilderness, there were Beth Arabah, Middin, Secacah,
Biranen da suke a jeji kuwa su ne, Bet-Araba, Middin, Sekaka,
62 Nibshan, the City of Salt, and En Gedi. These were six cities, including their villages.
Nibshan, Birnin gishiri da En Gedi, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
63 But as for the Jebusites, the inhabitants of Jerusalem, the tribe of Judah could not drive them out, so the Jebusites live there with the tribe of Judah to this day.
Kabilar Yahuda kuwa ba su iya korar Yebusiyawa waɗanda suke zama cikin Urushalima ba; har wa yau Yebusiyawa suna nan zaune tare da mutanen Yahuda.

< Joshua 15 >