< John 10 >

1 “Truly, truly, I say to you, he who does not enter through the gate into the sheep pen, but climbs up some other way, that man is a thief and a robber.
“Gaskiya nake gaya muku, mutumin da bai shiga inda ake ajiye garken tumaki ta ƙofa ba, amma ya hau ta katanga, ɓarawo ne, ɗan fashi kuma.
2 He who enters through the gate is the shepherd of the sheep.
Mutumin da ya shiga ta ƙofa makiyayin tumakinsa ne.
3 The gatekeeper opens for him. The sheep hear his voice, and he calls his own sheep by name and leads them out.
Mai gadin yakan buɗe wa makiyayin ƙofa, tumakin kuma sukan saurari muryarsa. Yakan kira tumakinsa da suna, yă kuma fid da su waje.
4 When he has brought out all his own, he goes ahead of them, and the sheep follow him, for they know his voice.
Sa’ad da ya fitar da dukan nasa waje, sai ya ja gabansu, tumakinsa kuma sukan bi shi domin sun san muryarsa.
5 They will not follow a stranger but instead they will avoid him, for they do not know the voice of strangers.”
Amma ba za su taɓa bin baƙo ba; sai dai ma su guje masa don ba su san muryar baƙo ba.”
6 Jesus spoke this parable to them, but they did not understand what these things were that he was saying to them.
Yesu ya yi musu wannan misali, amma ba su fahimci abin da yake faɗa musu ba.
7 Then Jesus said to them again, “Truly, truly, I say to you, I am the gate of the sheep.
Saboda haka Yesu ya sāke cewa, “Gaskiya nake gaya muku, ni ne ƙofar tumakin.
8 Everyone who came before me is a thief and a robber, but the sheep did not listen to them.
Duk waɗanda suka riga ni zuwa ɓarayi ne,’yan fashi kuma, amma tumakin ba su saurare su ba.
9 I am the gate. If anyone enters in through me, he will be saved; he will go in and out and will find pasture.
Ni ne ƙofar; duk wanda ya shiga ta wurina zai sami ceto. Zai riƙa shiga yă fita yă kuwa sami wurin kiwo.
10 The thief does not come if he would not steal and kill and destroy. I have come so that they will have life and have it abundantly.
Ɓarawo yakan zo don yă yi sata ne kawai da kisa da kuma ɓarna. Ni kuwa na zo ne don su sami rai, su kuma same shi a yalwace.
11 I am the good shepherd. The good shepherd lays down his life for the sheep.
“Ni ne makiyayi mai kyau. Makiyayi mai kyau yakan ba da ransa domin tumakin.
12 The hired servant is not a shepherd and does not own the sheep. He sees the wolf coming and abandons the sheep and escapes, and the wolf carries them off and scatters them.
Wanda aka ɗauko haya ba shi ne makiyayi mai tumakin ba. Saboda haka sa’ad da ya ga kyarkeci yana zuwa, sai yă sheƙa da gudu yă bar tumakin. Sai kyarkecin yă kai wa garken hari, yă kuma watsar da su.
13 He runs away because he is a hired servant and does not care for the sheep.
Mutumin yakan gudu don shi ɗan haya ne kawai, bai kuwa damu da tumakin ba.
14 I am the good shepherd, and I know my own, and my own know me.
“Ni ne makiyayi mai kyau; na san tumakina, tumakina kuma sun san ni,
15 The Father knows me, and I know the Father, and I lay down my life for the sheep.
kamar yadda Uba ya san ni, ni kuma na san Uba, ina kuwa ba da raina domin tumakin.
16 I have other sheep that are not of this sheep pen. I must bring them also, and they will hear my voice so that there will be one flock and one shepherd.
Ina da waɗansu tumaki da ba na wannan garken ba ne. Dole ne in kawo su su ma. Za su saurari muryata, za su kasance garke guda ɗaya, makiyayi guda kuma.
17 This is why the Father loves me: I lay down my life so that I may take it again.
Abin da ya sa Ubana yake ƙaunata ke nan, domin ina ba da raina, in ɗauko shi kuma.
18 No one takes it away from me, but I lay it down of myself. I have authority to lay it down, and I have authority to take it up again. I have received this command from my Father.”
Ba mai karɓe mini rai, ina dai ba da shi. Ina da iko in ba da shi, ina da iko in ɗauko shi kuma. Wannan umarni kuwa daga wurin Ubana na karɓo shi.”
19 A division again occurred among the Jews because of these words.
Saboda waɗannan kalmomi fa, sai ɓaraka ta sāke shiga cikin Yahudawa.
20 Many of them said, “He has a demon and is insane. Why do you listen to him?”
Da yawa daga cikinsu suka ce, “Yana da aljani, yana kuma hauka. Don me za ku saurare shi?”
21 Others said, “These are not the words of a demon-possessed man. Can a demon open the eyes of the blind?”
Amma waɗansu suka ce, “Kai, waɗannan kalmomi ba na mai aljani ba ne. Anya, aljani yana iya buɗe idanun makaho?”
22 Then it was time for the Festival of the Dedication in Jerusalem.
Bikin Miƙawa a Urushalima ya kewayo, lokacin sanyin hunturu ne kuwa.
23 It was winter, and Jesus was walking in the temple in the porch of Solomon.
Sai ga Yesu a filin haikali yana zagawa a Shirayin Solomon,
24 Then the Jews surrounded him and said to him, “How long will you hold us doubting? If you are the Christ, tell us openly.”
sai Yahudawa suka taru kewaye da shi, suka ce masa, “Har yaushe za ka bar mu da shakka? In kai ne Kiristin, ka faɗa mana a fili mana.”
25 Jesus replied to them, “I told you, but you do not believe. The works that I do in the name of my Father, these testify concerning me.
Yesu ya amsa ya ce, “Na faɗa muku, amma ba ku gaskata ba. Ayyukan da nake yi cikin sunan Ubana su suke nuna ko wane ne ni.
26 Yet you do not believe because you are not my sheep.
Amma ba ku gaskata ba domin ku ba tumakina ba ne.
27 My sheep hear my voice; I know them, and they follow me.
Tumakina sukan saurari muryata; na sansu, suna kuma bi na.
28 I give them eternal life; they will never die, and no one will snatch them out of my hand. (aiōn g165, aiōnios g166)
Ina ba su rai madawwami, ba za su taɓa hallaka ba; ba kuma mai ƙwace su daga hannuna. (aiōn g165, aiōnios g166)
29 My Father, who has given them to me, is greater than all others, and no one is able to snatch them out of the hand of the Father.
Ubana, wanda ya ba ni su, ya fi duka girma, ba mai ƙwace su daga hannun Ubana.
30 I and the Father are one.”
Da ni da Uba ɗaya ne.”
31 Then the Jews took up stones again to stone him.
Sai Yahudawa suka sāke ɗebo duwatsu don su jajjefe shi,
32 Jesus answered them, “I have shown you many good works from the Father. For which of those works are you stoning me?”
amma Yesu ya ce musu, “Na nuna muku ayyukan alheri masu yawa da Uba ya aiko ni in yi, a kan wanne kuke so ku jajjefe ni?”
33 The Jews answered him, “We are not stoning you for any good work, but for blasphemy, because you, a man, are making yourself God.”
Yahudawa suka amsa suka ce, “Ai, ba don wani daga cikin waɗannan ayyukan alheri ne muke so mu jajjefe ka ba, amma don saɓon da kake yi, kai da kake mutum kawai, kana mai da kanka Allah.”
34 Jesus answered them, “Is it not written in your law, 'I said, “You are gods”'?
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ba a rubuce yake a cikin Dokarku ba cewa, ‘Na ce ku alloli ne’?
35 If he called them gods, to whom the word of God came (and the scripture cannot be broken),
Mun dai san Nassi ba ya ƙarya, In har ya kira su waɗanda maganar Allah ta zo musu, ‘alloli,’
36 do you say to him whom the Father set apart and sent into the world, 'You are blaspheming,' because I said, 'I am the Son of God'?
to, game da wanda Uba ya keɓe a matsayin nasa ne ya kuma aiko shi duniya. Don me kuke ce saɓo nake, domin na ce, ‘Ni Ɗan Allah ne?’
37 If I am not doing the works of my Father, do not believe me.
In ba ayyukan da Ubana yake yi ne nake yi ba, to, kada ku gaskata ni.
38 But if I am doing them, even if you do not believe me, believe in the works so that you may know and understand that the Father is in me and that I am in the Father.”
Amma in su nake yi, ko ba ku gaskata ni ba, to, ku gaskata ayyukan, don ku sani, ku kuma gane, Uban yana cikina, ni kuma ina cikin Uban.”
39 They tried to seize him again, but he went away out of their hand.
Sai suka sāke yin ƙoƙari su kama shi, amma ya kuɓuce musu.
40 He went away again beyond the Jordan to the place where John had first been baptizing, and he stayed there.
Sa’an nan Yesu ya sāke koma ƙetaren Urdun inda dā Yohanna yake baftisma. A can ya zauna
41 Many people came to him and they said, “John indeed did no signs, but all the things that John has said about this man are true.”
mutane da yawa suka zo wurinsa. Suka ce, “Ko da yake Yohanna bai yi wani abin banmamaki ba, duk abubuwan da Yohanna ya faɗa game da mutumin nan gaskiya ne.”
42 Many people believed in him there.
A nan kuwa mutane da yawa suka gaskata da Yesu.

< John 10 >