< Job 3 >

1 After this, Job opened his mouth and cursed the day he was born.
Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
2 He said,
Ayuba ya ce,
3 “May the day on which I was born perish, the night that said, 'A boy has been conceived.'
“A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
4 May that day be dark; may not God from above call it to mind, neither may the sun shine on it.
Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
5 May darkness and the shadow of death claim it for their own. May a cloud live over it; may everything that makes the day black truly terrify it.
Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
6 As for that night, may thick darkness seize it. May it not rejoice among the days of the year; may it not come into the number of the months.
Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
7 See, may that night be barren; may no joyful voice come into it.
Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
8 May they curse that day, those who know how to wake up Leviathan.
Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
9 May the stars of that day's dawn be dark. May that day look for light, but find none; neither may it see the eyelids of the dawn,
Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
10 because it did not shut up the doors of my mother's womb, and because it did not hide trouble from my eyes.
gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
11 Why did I not die when I came out from the womb? Why did I not give up my spirit when my mother bore me?
“Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
12 Why did her knees welcome me? Why did her breasts receive me so that I should suck?
Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
13 For now I would have been lying down quietly. I would have slept and been at rest
Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
14 with kings and counselors of the earth, who built up tombs for themselves that are now in ruins.
tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
15 Or I would have been lying with princes who once had gold, who had filled their houses with silver.
da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
16 Or perhaps I would have been stillborn, like infants that never see the light.
Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
17 There the wicked cease from trouble; there the weary are at rest.
A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
18 There the prisoners are at ease together; they do not hear the voice of the slave driver.
Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
19 Both small and great people are there; the servant is free from his master there.
Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
20 Why is light given to him who is in misery? Why is life given to the one who is bitter in soul,
“Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
21 to one who longs for death without it coming; to one who digs for death more than for hidden treasure?
ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
22 Why is light given to one who rejoices very much and is glad when he finds the grave?
waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
23 Why is light given to a man whose way is hidden, a man whom God has hedged in?
Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
24 For my sighing happens instead of eating; my groaning is poured out like water.
Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
25 For the thing that I feared has come on me; what I was afraid of has come to me.
Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
26 I am not at ease, I am not quiet, and I have no rest; trouble comes instead.”
Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”

< Job 3 >