< Job 14 >

1 Man, who is born of woman, lives only a few days and is full of trouble.
“Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
2 He sprouts from the ground like a flower and is cut down; he flees like a shadow and does not last.
Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
3 Do you look at any of these? Do you bring me into judgment with you?
Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
4 Who can bring something clean out of something unclean? No one.
Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
5 Man's days are determined. The number of his months is with you; you have appointed his limits that he cannot pass.
An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
6 Look away from him that he may rest, so that he may enjoy his day like a hired man if he can do so.
Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
7 There can be hope for a tree; if it is cut down, it might sprout again, so that its tender stalk does not disappear.
“Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
8 Though its root grows old in the earth, and its stump dies in the ground,
Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
9 yet even if it only smells water, it will bud and send out branches like a plant.
Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
10 But man dies; he becomes weak; indeed, man stops breathing, and then where is he?
Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
11 As water disappears from a lake, and as a river loses water and dries up,
Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
12 so people lie down and do not rise again. Until the heavens are no more, they will not awake nor be roused out of their sleep.
haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
13 Oh, that you would hide me away in Sheol away from troubles, and that you would keep me in private until your wrath is over, that you would set me a fixed time to stay there and then call me to mind! (Sheol h7585)
“Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
14 If a man dies, will he live again? If so, I would wish to wait all my weary time there until my release should come.
In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
15 You would call, and I would answer you. You would have a desire for the work of your hands.
Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
16 You would number and care for my footsteps; you would not keep track of my sin.
Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
17 My transgression would be sealed up in a bag; you would cover up my iniquity.
Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
18 But even mountains fall and come to nothing; even rocks are moved out of their place;
“Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
19 the waters wear down the stones; their flooding washes away the dust of the earth. Like this, you destroy the hope of man.
yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
20 You always defeat him, and he passes away; you change his face and send him away to die.
Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
21 If his sons are honored, he does not know it; and if they are brought low, he does not see it.
Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
22 He feels only the pain of his own body, and he mourns for himself.
Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”

< Job 14 >