< Jeremiah 41 >
1 But it happened that in the seventh month Ishmael son of Nethaniah son of Elishama, from the royal family, and some officers of the king, came—ten men were with him—to Gedaliah son of Ahikam, at Mizpah. They ate food together there in Mizpah.
A wata na goma sha bakwai sai Ishmayel ɗan Netaniya, ɗan Elishama, wanda yake mai jinin sarauta yake kuma ɗaya daga cikin hafsoshin sarki, ya zo tare da mutum goma wurin Gedaliya ɗan Ahikam a Mizfa. Yayinda suke ci tare a can,
2 But Ishmael son of Nethaniah, and the ten men who were with him rose up and attacked Gedaliah son of Ahikam son of Shaphan, with the sword. Ishmael killed Gedaliah, whom the king of Babylon had put in charge of the land.
sai Ishmayel ɗan Netaniya da mutum goma waɗanda suke tare da shi suka kashe Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, da takobi, suka kashe wannan da sarkin Babilon ya naɗa a matsayin gwamna a kan ƙasar.
3 Then Ishmael killed all the Judeans who were with Gedaliah in Mizpah and the Chaldean fighting men found there.
Ishmayel ya kuma kashe dukan Yahudawan da suke tare da Gedaliya a Mizfa, haka ma ya yi da sojojin Babiloniyawan da suke can.
4 Then it was the second day after the killing of Gedaliah, but no one knew.
Kashegari bayan an kashe Gedaliya, kafin wani ya san abin da ya faru,
5 Some men came from Shechem, from Shiloh, and from Samaria—eighty men who had shaved their beard, torn their clothes, and cut themselves—with food offerings and frankincense in their hands to go to Yahweh's house.
sai ga mutane tamanin daga Shekem, Shilo da Samariya suka zo da gemunsu a aske, da tufafinsu a kece, da jikunansu a tsage, suka kawo hadayun gari da turare tare da su a gidan Ubangiji.
6 So Ishmael son of Nethaniah went out from Mizpah to meet them as they went, walking and weeping. Then it happened that as he encountered them, he said to them, “Come to Gedaliah son of Ahikam!”
Ishmayel ɗan Netaniya ya fito daga Mizfa don yă sadu da su. Sa’ad da ya sadu da su, sai ya ce, “Ku zo wurin Gedaliya ɗan Ahikam.”
7 It came about that when they came into the city, Ishmael son of Nethaniah slaughtered them and threw them into a pit, he and the men who were with him.
Da suka shiga cikin birni, sai Ishmayel ɗan Netaniya da mutanen da suke tare da shi suka karkashe su suka zubar a rijiya.
8 But there were ten men among them who said to Ishmael, “Do not kill us, for there are provisions of ours in a field: Wheat and barley, oil and honey.” So he did not kill them with their other companions.
Amma goma daga cikinsu suka ce wa Ishmayel, “Kada ka kashe mu, muna da alkama da sha’ir, mai da kuma zuma, a ɓoye a gona.” Saboda haka ka bar mu kada ka kashe mu tare da sauran.
9 The cistern where Ishmael threw all the dead bodies that he had killed, was a large cistern that King Asa dug to make a defense against King Baasha of Israel. Ishmael son of Nethaniah filled it in with the dead.
To, rijiyar da ya zubar da gawawwakin mutanen da ya kashe tare da ta Gedaliya ita ce wadda Sarki Asa ya haƙa a matsayin kāriya saboda Ba’asha sarkin Isra’ila. Ishmayel ɗan Netaniya ya cika ta da gawawwaki.
10 Next Ishmael captured all the other people who were in Mizpah, the king's daughters and all the people who were left in Mizpah whom Nebuzaradan the chief guard had assigned to Gedaliah son of Ahikam. So Ishmael son of Nethaniah captured them and went to cross over to the people of Ammon.
Ishmayel ya mai da dukan sauran mutanen da suke Mizfa bayi’ya’yan sarki mata tare da dukan sauran da aka bari a can, waɗanda Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya bari a hannun Gedaliya ɗan Ahikam. Ishmayel ɗan Netaniya ya kwashe su ganima, ya tashi don yă haye zuwa wurin Ammonawa.
11 But Johanan son of Kareah and all the army commanders with him heard of all the harm that Ishmael son of Nethaniah had done.
Sa’ad da Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojojin da suke tare da shi suka ji dukan laifofin da Ishmayel ɗan Netaniya ya aikata,
12 So they took all their men and went to fight against Ishmael son of Nethaniah. They found him at the great pool of Gibeon.
sai suka kwashe dukan mutanensu suka tafi don su yaƙi Ishmayel ɗan Netaniya. Suka iske shi kusa da babban tafki a Gibeyon.
13 Then it happened that when all the people who were with Ishmael saw Johanan son of Kareah and all the army commanders who were with him, they were very happy.
Sa’ad da dukan mutanen da suke tare da Ishmayel suka ga Yohanan ɗan Kareya da shugabannin sojojin da suke tare da shi, sai suka yi farin ciki.
14 So all the people whom Ishmael had captured at Mizpah turned around and went to Johanan son of Kareah.
Dukan mutanen da Ishmayel ya kame a Mizfa suka juya, suka tafi wurin Yohanan ɗan Kareya.
15 But Ishmael son of Nethaniah fled with eight men from Johanan. He went to the people of Ammon.
Amma Ishmayel ɗan Netaniya da mutanensa takwas suka tsere daga Yohanan suka gudu zuwa wurin Ammonawa.
16 Johanan son of Kareah and all the army commanders with him took from Mizpah all the people who had been rescued from Ishmael son of Nethaniah. This was after Ishmael had killed Gedaliah son of Ahikam. Johanan and his companions took the strong men, the fighting men, the women and children, and the eunuchs who had been rescued at Gibeon.
Sai Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojojin da suke tare da shi suka bi da dukan waɗanda suka tsira daga Mizfa waɗanda ya karɓe daga Ishmayel ɗan Netaniya bayan ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wato, sojoji, mata, yara da fadawan da ya kawo daga Gibeyon
17 Then they went and stayed for a while in Geruth Kimham, which is near Bethlehem. They were going to go to Egypt
Sai suka ci gaba, suka dakata a Gerut Kimham kusa da Betlehem a kan hanyarsu zuwa Masar
18 because of the Chaldeans. They were afraid of them since Ishmael son of Nethaniah had killed Gedaliah son of Ahikam, whom the king of Babylon had put in charge of the land.
don su kuɓuce wa Babiloniyawa. Sun ji tsoronsu domin Ishmayel ɗan Netaniya ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wanda sarkin Babilon ya naɗa gwamna a kan ƙasar.